• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ‘yan jarida da su guji tallata ’yan ta’adda da ‘yan bindiga da sauran miyagu da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasar nan.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin zama na bakwai na Jerin Zauren Bayanai na Ministoci na shekarar 2025 wanda aka gudanar a Cibiyar Yaɗa Labarai ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Jirgin Farko Daga Minna Zuwa Abuja Ya Nuna Haɗin Gwiwar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi – Minista
  • Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Idris ya ce, “Kafofin yaɗa labarai, a matsayin su na masu tantance labarai kuma abokan hulɗa wajen gina ƙasa, suna da muhimmiyar rawar da za su taka wajen ƙarfafa gwiwar dakarun mu ta hanyar nuna irin nasarorin da suka samu da sadaukarwar da suke yi.

“Dole ne mu guji tallata waɗannan ƙungiyoyi. Dole ne mu cire su daga shafukan farko na jaridu, mu riƙa bayar da rahoto a kan su daidai da yadda suke — wato masu laifi ne — ba tare da ƙawata ayyukan su ko ba da muhimmanci ga ƙarya da farfagandar da suke yaɗawa ba.”

Ministan ya ƙara da cewa ‘yan ta’adda da sauran miyagun ƙungiyoyi suna amfani da kafafen watsa labarai da na sada zumunta ne domin su yaɗa fargaba da ƙarya da kuma jawo mutane zuwa gare su.

Labarai Masu Nasaba

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

Saboda haka, ya buƙaci ’yan jarida da editoci da su zama masu kishin ƙasa da ƙwarewa wajen bayar da rahoto, ta hanyar guje wa manyan kanun labarai masu tayar da hankali da kuma ƙin zama hanyar yaɗa farfaganda ta masu aikata ta’addanci.

Ya ce: “Waɗannan ba ‘yan gwagwarmayar ‘yanci ba ne; masu kisa ne, masu sace mutane ne, masu ɓarna ne, kuma dole ne a bayyana su a hakan.”

Ministan ya kuma haskaka wani muhimmin ɓangare na Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, musamman ɓangaren da ya shafi “Ƙarfafa Tsaron Ƙasa Don Samar Da Zaman Lafiya Da Cigaba.”

Ya ce Gwamnatin Tarayya tana ci gaba da kashe kuɗi wajen samar da kayan aiki na zamani ga sojoji, da inganta binciken leƙen asiri da kuma haɓaka haɗin gwiwa da ƙasashen duniya.

Idris ya bayyana cewa Jerin Zauren Bayanai na Ministocin wani shiri ne da ma’aikatar sa ta ƙirƙira domin bai wa ministoci dama su faɗa wa ’yan Nijeriya irin nasarorin da suke samu, da ayyukan da ke gudana da kuma tsare-tsaren da za su aiwatar a nan gaba.

Ya ce, “Ta wannan dandali na tattaunawa, wanda ake watsawa kai-tsaye a tashoshin talbijin na ƙasa da kuma kafafen sada zumunta, muna ci gaba da nuna jajircewar mu ga gaskiya, ɗaukar nauyi, da haɗin kai da jama’a.”

Ministan ya yaba wa kafafen yaɗa labarai bisa goyon bayan da suke ba wannan shiri da kuma rawar da suke takawa wajen wayar da kan al’umma game da ayyukan gwamnati.

A taron, Ministan Tsaro, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, da Ministan Muhalli, Alhaji Balarabe Abbas, sun gabatar da bayanai ga manema labarai kan nasarorin da ma’aikatun su suke samu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Tattaunawar Cinikayya Da Za A Yi Tsakanin Babban Jami’inta Da Na Amurka

Next Post

Duniya Ta Gano Damammaki Masu Kyau Daga Kasuwar Kasar Sin A Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Ta Duniya

Related

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

2 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

4 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

13 hours ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

14 hours ago
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
Labarai

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

16 hours ago
Next Post
Duniya Ta Gano Damammaki Masu Kyau Daga Kasuwar Kasar Sin A Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Ta Duniya

Duniya Ta Gano Damammaki Masu Kyau Daga Kasuwar Kasar Sin A Yayin Hutun Ranar Ma’aikata Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.