• English
  • Business News
Sunday, October 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari

by Muhammad
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bukaci ‘Yan Nijeriya da su fito kwansu da kwarkwatarsu su zabi dan takarar Jam’iyyarsa ta APC a zaben shugaban kasa da zai gudanar ranar 25, ga Febarairun nan.

Shugaba Buhari ya yi wannan kiran ga ‘Yan Nijeriya ta hanyar wallafa sakon a shafinsa na kafar sada zumunta na Facebook a yammacin ranar Lahadin nan.

  • Ganduje Ya Maka Buhari A Kotun Koli Kan Batu Canjin Kudi 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Wa Da El-rufai Martani Kan Zargin Yi Wa Tunibu Zagon Kasa

Shugaba Buharin yabayya cewa, “Zuwa ga ’Yan Nijeriya, ina so in yi amfani da wannan dama domin in sake gode muku da kuka zabe ni har na zama shugaban kasa har sau biyu a jere.”

“A yanzu ni ba dan takara ba ne a wannan zaben, amma jam’iyyata ta APC tana da dan takara wato, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu,”

“Kamar yadda na ambata a baya, Tinubu mutum ne amintacce kuma mai gaskiya mai son Nijeriya, da kaunar ci gaban Jama’a da kasarmu,”

LABARAI MASU NASABA

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

“Ina kira gare ku da ku zabi, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Saboda mun gamsu da shi kuma na yi imani zai dora kan irin nasarorin da muka samu,”

“A karshe ina kara tabbatar muku da cewa ina da cikakkiyar masaniyar irin wahalhalun da kuke fuskanta a halin yanzu sakamakon wasu cikin manufofin gwamnati da ake aiwatarwa a yanzu da nufin kawo ci gaba a kasa baki daya,”

“Ina rokon ku da ku kara hakuri yayin da muke daukar matakan da suka dace don rage wahalhalu. In sha Allahu za a samu alheri a karshen lamarin.” a cewarsa.

Yanzu dai abun jira a gani shi ne, shin ko ‘Yan Nijeriya za su amsa kiran na shugaban kasar wurin zabar Tunibun?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
Siyasa

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

October 11, 2025
Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

October 11, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
‘Rikicin Sauya Kudi’: Adamu Da Gwamnonin APC Sun Shiga Taron Gaggawa Na Sirri A Abuja

‘Rikicin Sauya Kudi’: Adamu Da Gwamnonin APC Sun Shiga Taron Gaggawa Na Sirri A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

October 11, 2025
Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

October 11, 2025
Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

October 11, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

October 11, 2025
Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

October 11, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.