ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Maka Buhari A Kotun Koli Kan Batu Canjin Kudi 

by Sadiq
3 years ago
Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje

Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano ya maka Shugaba Muhammadu Buhari kara a gaban Kotun Koli kan sauya fasalin da aka yi wa takardun naira.

A watan Oktoban bara ne dai Babban Bankin Najeriya CBN bisa amincewar Shugaba Buhari ya sauya fasalin wasu daga cikin manyan kudin kasar na naira 200 da 500 da 1,000.

  • APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano
  • Bayan Shafe Shekaru 32 Yana Limanci A Harami Sheikh Shuraim, Ya Nemi Uzurin Ajiye Limancin

A karar mai lamba SC/CS/200/2023 wadda Babban Lauyan Jihar Kano ya shigar ta hannun Sunusi Musa, Babban Lauya a Najeriya (SAN), Gwamnatin Kano ta ayyana cewa Shugaba Buhari shi kadai ba shi da hurumin umartar CBN dakatar da tsoffin takardun kudin da aka sauyawa fasali.

ADVERTISEMENT

Aminiya ta ruwaito cewa, karar wadda Gwamnatin Kano ta gabatar a jiya Alhamis, ta kafa hujjar cewa Buhari ba shi da wannan hurumi ba tare da tuntuba da amincewar Majalisar Tattalin Arziki da kuma Majalisar Zartarwa ta kasar ba.

A bisa wannan madogara ce Gwamnatin Kano ta bukaci Kotun Kolin ta soke matakin Babban Bankin na janye takardun kudaden saboda abin ta kira wahalar da al’ummar jihar ke ciki.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A tattaunawarsa da manema labarai, Babban Lauyan da ya shigar da karar Sunusi Musa ya ce a ranar Laraba ne kotun za ta saurari karar.

Kazalika, Gwamnatin Kanon tana son kotun ta bayar da umarnin da zai tilasta wa Gwamnatin Tarayya ta soke shirin nata na sauyin kudi saboda a cewarta ya saba wa Kundin Tsarin Mulkin Kasar na 1999.

An kuma ruwaito cewa Gwamnatin Kanon tana bukatar Kotun Kolin ta zartar cewa umarnin da Shugaba Buhari ya bai wa CBN na takaita yawan kudin da jama’a za su fitar daga asusunsu na banki ba tare da tuntubar Majalisar Tattalin Arziki da kuma ta Zartarwa ba, abu ne da ya saba wa tsarin mulki da saba wa doka a don haka ba shi da iko.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Tawagar Ba Da Tallafin Jiyya Ta Sin Dake Afrika Ta Tsakiya

Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Tawagar Ba Da Tallafin Jiyya Ta Sin Dake Afrika Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.