ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Rikicin Sauya Kudi’: Adamu Da Gwamnonin APC Sun Shiga Taron Gaggawa Na Sirri A Abuja

by Muhammad
3 years ago
APC

Ana ci gaba da wani taron gaggawa na gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ne ya kira taron domin tattauna batutuwan da suka shafi yakin neman zabe, rikicin Naira da kuma zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a yi a ranar Asabar mai zuwa.

  • Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari
  • Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Wa Da El-rufai Martani Kan Zargin Yi Wa Tunibu Zagon Kasa

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen sakatariyar yayin da ake ci gaba da gudanar da taron na sirri.

ADVERTISEMENT

Gwamna Nasir El-Rufai (Kaduna), Abdullahi Sule (Nasarawa), Bello Matawalle (Zamfara) da Simon Lalong (Plateau) da kuma Mai Mala Buni (Yobe) na daga cikin gwamnonin da suka halarci taron.

A jawabinsa na bude taron, Adamu ya ce, “Na yi farin ciki da amsar da aka bayar kawo yanzu. Kuma ni a fahimtata da yawa daga cikin gwamnonin suna kan hanyarsu ta zuwa. Nasan kuna sane da dalilan da suka wajabta buƙatar wannan gayyata sakamakon yadda lamura suke tafiya a yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

“Ba ma son zama a yanke hukunci ga kowa ko hukumomi game da abin da ke faruwa a kasar a yau kamar yadda lamarin ya shafi babbar jam’iyyarmu.

“Na ga abin da ya fi dacewa a yi shi ne a samu duk masu rike da madafun iko a cikin jam’iyya, mu hadu a yi mu’amala da juna ta yadda za mu iya samun kyakkyawar matsaya don magance yanayin da muke ciki.”

Wasu gwamnonin jam’iyyar APC sun shigar da kara a gaban gwamnatin tarayya kan batun sake fasalin naira.

Kotun koli ta umarci CBN da kada ya aiwatar da wa’adin amma Godwin Emefiele, gwamnan CBN ya ce babu bukatar a canza wa’adin.

Buhari dai ya bi umarnin kotu ta wani bangare bayan da ya bayar da umarnin tsawaita wa’adin Naira 200 tare da bayyana cewa tsofaffin takardun N500 da N1000 a dakatar da karbarsu.

Hakan ya jawo cece-kuce a fadin kasar. Gwamnonin jam’iyya mai mulki sun bi sahun masu sukar Buhari kan lamarin.

Yayin da Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano ya yi zargin cewa manufar sake fasalin Naira na da nufin durkusar da dimokuradiyyar Nijeriya, takwaransa na Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bukaci mazauna yankin da su yi watsi da umarnin Buhari.

Gwamna Dapo Abidoun (Ogun) da Babajide Sanwo-Olu (Lagos), Abubakar Badaru (Jigawa) na daga cikin wadanda suka bayyana cewa har yanzu ana amfani da tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 a jihohinsu.

APC
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Wace Fa’ida AfCFTA Za Ta Haifar Wa Najeriya?

Wace Fa’ida AfCFTA Za Ta Haifar Wa Najeriya?

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.