ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Rikicin Sauya Kudi’: Adamu Da Gwamnonin APC Sun Shiga Taron Gaggawa Na Sirri A Abuja

by Muhammad
3 years ago
APC

Ana ci gaba da wani taron gaggawa na gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ne ya kira taron domin tattauna batutuwan da suka shafi yakin neman zabe, rikicin Naira da kuma zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a yi a ranar Asabar mai zuwa.

  • Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari
  • Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Wa Da El-rufai Martani Kan Zargin Yi Wa Tunibu Zagon Kasa

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen sakatariyar yayin da ake ci gaba da gudanar da taron na sirri.

ADVERTISEMENT

Gwamna Nasir El-Rufai (Kaduna), Abdullahi Sule (Nasarawa), Bello Matawalle (Zamfara) da Simon Lalong (Plateau) da kuma Mai Mala Buni (Yobe) na daga cikin gwamnonin da suka halarci taron.

A jawabinsa na bude taron, Adamu ya ce, “Na yi farin ciki da amsar da aka bayar kawo yanzu. Kuma ni a fahimtata da yawa daga cikin gwamnonin suna kan hanyarsu ta zuwa. Nasan kuna sane da dalilan da suka wajabta buƙatar wannan gayyata sakamakon yadda lamura suke tafiya a yanzu.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Ba ma son zama a yanke hukunci ga kowa ko hukumomi game da abin da ke faruwa a kasar a yau kamar yadda lamarin ya shafi babbar jam’iyyarmu.

“Na ga abin da ya fi dacewa a yi shi ne a samu duk masu rike da madafun iko a cikin jam’iyya, mu hadu a yi mu’amala da juna ta yadda za mu iya samun kyakkyawar matsaya don magance yanayin da muke ciki.”

Wasu gwamnonin jam’iyyar APC sun shigar da kara a gaban gwamnatin tarayya kan batun sake fasalin naira.

Kotun koli ta umarci CBN da kada ya aiwatar da wa’adin amma Godwin Emefiele, gwamnan CBN ya ce babu bukatar a canza wa’adin.

Buhari dai ya bi umarnin kotu ta wani bangare bayan da ya bayar da umarnin tsawaita wa’adin Naira 200 tare da bayyana cewa tsofaffin takardun N500 da N1000 a dakatar da karbarsu.

Hakan ya jawo cece-kuce a fadin kasar. Gwamnonin jam’iyya mai mulki sun bi sahun masu sukar Buhari kan lamarin.

Yayin da Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano ya yi zargin cewa manufar sake fasalin Naira na da nufin durkusar da dimokuradiyyar Nijeriya, takwaransa na Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bukaci mazauna yankin da su yi watsi da umarnin Buhari.

Gwamna Dapo Abidoun (Ogun) da Babajide Sanwo-Olu (Lagos), Abubakar Badaru (Jigawa) na daga cikin wadanda suka bayyana cewa har yanzu ana amfani da tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 a jihohinsu.

APC
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Wace Fa’ida AfCFTA Za Ta Haifar Wa Najeriya?

Wace Fa’ida AfCFTA Za Ta Haifar Wa Najeriya?

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.