• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudirin Sake Fasalin Haraji Ya Raba Kan ‘Yan Majalisar Arewa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kudirin zartaswa da ke gaban majalisun tarayya guda biyu na dokar sake fasalin haraji ya raba kan ‘yan majalisa daga yankin arewacin kasar nan.

 

Tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Ali Ndume a wata sanarwa da ya fitar a baya-bayan nan ya goyi bayan gwamnonin arewa da kungiyar tuntuba ta arewa (ACF), wadanda a tarurruka daban-daban suka yi watsi da kudirin dokar.

  • Katsewar Lantarki: Masu Masana’antu Sun Kashe Naira Biliyan 238.3 Wajen Samun Wuta
  • Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Ndume a cikin sanarwar ya yi nuni da cewa, manufofin tattalin arziki na gwamnati mai ci sun talautar da al’umma, sannan kuma ya yi ikirarin cewa sake fasalin harajin zai kara wa talakawan Nijeriya matsin tattalin arziki.

 

Labarai Masu Nasaba

GORON JUMA’A 09/05/2025

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

Ya ce, “Wannan harajin da suke magana a kai, mun kusan rasa masu matsakaicin karfi a Nijeriya. Ko kana da shi ko ba ka da shi. Wadanda suke a tsakiya ana matse su. Idan ’yan Nijeriya za su iya biyan wadannan haraji, ba komai.

 

“Amma a halin da ake ciki yanzu, kara haraji ba mafita ba. Ba zan goyi bayan wani karin haraji ba.”

 

Sai dai da yake magana a ranar Litinin a Abuja, dan rajin kare hakkin Bil’adama kuma tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya a majalisar wakilai ta 8, Shehu Sani, ya yi ikirarin cewa Sanata Ndume da wasu da ke kalubalantar shirin garambawul na harajin da ake shirin yi ba magana ce ta ilimi ba.

 

Ya ci gaba da cewa arewa kamar sauran sassan kasar nan za su ci gajiyar wannan sauyi na haraji.

 

Ya dage kan cewa kudirorin sake fasalin harajin ba su shafi arewa ba kamar yadda Ndume da makarrabansa ke bayyanawa, amma arewa ta tsaya kyam wajen yin kwaskwarimar da za ta sanya harajin VAT a hannun kowace jiha don sarrafa shi.

 

Sani ya ce wannan garambawul na iya haifar da sauyi daga tsarin haraji na baya da kuma sabon tsarin samar da kudaden shiga, domin zai magance matsalolin ‘yan kasuwa da za su iya yin duk wani abu don kaucewa kudaden haraji da kuma neman hana harajin da ba dole ba.

 

Ya yi gargadin cewa tattalin arzikin kasar zai yi matukar kaduwa idan aka soke kudirorin gyara haraji, inda ya yi Allah-wadai da kin amincewar da gwamnonin jihohin arewa suka yi na sake fasalin. Ya shawarci gwamnonin jihohin da su sa masu ba da shawara su yi nazari a kan kudirin, idan ba su da lokacin yin shi da kansu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mizanin Hajoji Da Hidimomi Da Masana’antun Kasar Sin Ke Samarwa Ya Karu Da Kaso 5.3 Bisa Dari A Watan Oktoba

Next Post

An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

Related

GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

33 minutes ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

2 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

3 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

4 hours ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

5 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

6 hours ago
Next Post
An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.