• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kugiyar Northwest Progressives Forum (NPF) ta yi watsi da cece-kucen da ake yi kan zabar tsohon gwamnan jihar Jigawa, Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro Nijeriya, inda ta ce shugaba Bola Tinubu ya dasa kwarya a gurbinta.

Da yake jawabi a taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna a ranar Laraba, Daraktan Sadarwa na kungiyar Adamu Isa, ya bayyana cewa, ya kamata masu sukar bai wa Badaru mukamin minista su yi biyayya ga hukuncin shugaba Tinubu.

  • Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?
  • Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Isa ya ce: “Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan mataki da ya dauka, duba da irin yadda Badaru yake da ban mamaki.”

Kungiyar ta bayyana cewa a lokacin da yake rike da mukamin Gwamnan Jihar Jigawa, ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, hakan ta sa ya yi nisa a harkokin tsaro.

Da yake karin haske game da cancantar Badaru ya bayyana cewar tsohon gwamnan ba ya bukatar horon soji don gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Adamu ya jaddada cewa tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya rike mukamin a baya kuma ya taka rawar gani a wancan lokaci.

NPF ta nuna farin cikinta kan rahotannin da ke cewa Badaru ya riga ya hada tawagar kwararru domin taimaka masa wajen gudanar da ayyukansa a matsayin babban ministan tsaro.

Adamu ya tabbatar da cewa, wannan mataki na taka-tsantsan yana kara jaddada kyakkyawan hangen nesa da basirar Badaru na hada tawaga mai inganci.

An kuma bayyana fahimtar kungiyar game da manufofin tsaron kasa, inda ta lissafo muhimman abubuwa da suka hada da tabbatar da shirye-shiryen rundunar sojojin Nijeriya ta kasa, ta ruwa da ta sama, daidaita makamai da ma’aikata don bukatun tsaro, da kuma ba da fifikon jin dadin dakarun soji ta hanyar bada horo.

NPF ta bayyana muhimmancin inganta fagen tsaron kasar nan don rage dogaro da kasashen ketare da tabbatar da hadin gwiwar tsaro a shiyyar da duniya baki daya.

Adamu ya kara da cewa, “Mun yi imani cewa nada Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro zai kawo sauyi mai tasiri.”

A karshe kungiyar ta bayyana kudirinta na marawa Badaru baya a aikinsa na kasa tare da yin alkawarin ci gaba da yi masa addu’a don samun nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadaruKungiyaMinistan TsaroNPFTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?

Next Post

CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

8 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

9 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

9 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

12 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

13 hours ago
Next Post
CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.