• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kugiyar Northwest Progressives Forum (NPF) ta yi watsi da cece-kucen da ake yi kan zabar tsohon gwamnan jihar Jigawa, Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro Nijeriya, inda ta ce shugaba Bola Tinubu ya dasa kwarya a gurbinta.

Da yake jawabi a taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna a ranar Laraba, Daraktan Sadarwa na kungiyar Adamu Isa, ya bayyana cewa, ya kamata masu sukar bai wa Badaru mukamin minista su yi biyayya ga hukuncin shugaba Tinubu.

  • Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?
  • Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Isa ya ce: “Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan mataki da ya dauka, duba da irin yadda Badaru yake da ban mamaki.”

Kungiyar ta bayyana cewa a lokacin da yake rike da mukamin Gwamnan Jihar Jigawa, ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, hakan ta sa ya yi nisa a harkokin tsaro.

Da yake karin haske game da cancantar Badaru ya bayyana cewar tsohon gwamnan ba ya bukatar horon soji don gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Adamu ya jaddada cewa tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya rike mukamin a baya kuma ya taka rawar gani a wancan lokaci.

NPF ta nuna farin cikinta kan rahotannin da ke cewa Badaru ya riga ya hada tawagar kwararru domin taimaka masa wajen gudanar da ayyukansa a matsayin babban ministan tsaro.

Adamu ya tabbatar da cewa, wannan mataki na taka-tsantsan yana kara jaddada kyakkyawan hangen nesa da basirar Badaru na hada tawaga mai inganci.

An kuma bayyana fahimtar kungiyar game da manufofin tsaron kasa, inda ta lissafo muhimman abubuwa da suka hada da tabbatar da shirye-shiryen rundunar sojojin Nijeriya ta kasa, ta ruwa da ta sama, daidaita makamai da ma’aikata don bukatun tsaro, da kuma ba da fifikon jin dadin dakarun soji ta hanyar bada horo.

NPF ta bayyana muhimmancin inganta fagen tsaron kasar nan don rage dogaro da kasashen ketare da tabbatar da hadin gwiwar tsaro a shiyyar da duniya baki daya.

Adamu ya kara da cewa, “Mun yi imani cewa nada Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro zai kawo sauyi mai tasiri.”

A karshe kungiyar ta bayyana kudirinta na marawa Badaru baya a aikinsa na kasa tare da yin alkawarin ci gaba da yi masa addu’a don samun nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadaruKungiyaMinistan TsaroNPFTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?

Next Post

CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

8 minutes ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

1 hour ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

2 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

7 hours ago
Badaru
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

7 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

8 hours ago
Next Post
CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.