ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro

by yahuzajere
3 years ago
Badaru

Kugiyar Northwest Progressives Forum (NPF) ta yi watsi da cece-kucen da ake yi kan zabar tsohon gwamnan jihar Jigawa, Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro Nijeriya, inda ta ce shugaba Bola Tinubu ya dasa kwarya a gurbinta.

Da yake jawabi a taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna a ranar Laraba, Daraktan Sadarwa na kungiyar Adamu Isa, ya bayyana cewa, ya kamata masu sukar bai wa Badaru mukamin minista su yi biyayya ga hukuncin shugaba Tinubu.

  • Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?
  • Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Isa ya ce: “Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan mataki da ya dauka, duba da irin yadda Badaru yake da ban mamaki.”

ADVERTISEMENT

Kungiyar ta bayyana cewa a lokacin da yake rike da mukamin Gwamnan Jihar Jigawa, ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, hakan ta sa ya yi nisa a harkokin tsaro.

Da yake karin haske game da cancantar Badaru ya bayyana cewar tsohon gwamnan ba ya bukatar horon soji don gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Adamu ya jaddada cewa tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya rike mukamin a baya kuma ya taka rawar gani a wancan lokaci.

NPF ta nuna farin cikinta kan rahotannin da ke cewa Badaru ya riga ya hada tawagar kwararru domin taimaka masa wajen gudanar da ayyukansa a matsayin babban ministan tsaro.

Adamu ya tabbatar da cewa, wannan mataki na taka-tsantsan yana kara jaddada kyakkyawan hangen nesa da basirar Badaru na hada tawaga mai inganci.

An kuma bayyana fahimtar kungiyar game da manufofin tsaron kasa, inda ta lissafo muhimman abubuwa da suka hada da tabbatar da shirye-shiryen rundunar sojojin Nijeriya ta kasa, ta ruwa da ta sama, daidaita makamai da ma’aikata don bukatun tsaro, da kuma ba da fifikon jin dadin dakarun soji ta hanyar bada horo.

NPF ta bayyana muhimmancin inganta fagen tsaron kasar nan don rage dogaro da kasashen ketare da tabbatar da hadin gwiwar tsaro a shiyyar da duniya baki daya.

Adamu ya kara da cewa, “Mun yi imani cewa nada Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro zai kawo sauyi mai tasiri.”

A karshe kungiyar ta bayyana kudirinta na marawa Badaru baya a aikinsa na kasa tare da yin alkawarin ci gaba da yi masa addu’a don samun nasara.

Badaru
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.