ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro

by yahuzajere
3 years ago
Badaru

Kugiyar Northwest Progressives Forum (NPF) ta yi watsi da cece-kucen da ake yi kan zabar tsohon gwamnan jihar Jigawa, Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro Nijeriya, inda ta ce shugaba Bola Tinubu ya dasa kwarya a gurbinta.

Da yake jawabi a taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna a ranar Laraba, Daraktan Sadarwa na kungiyar Adamu Isa, ya bayyana cewa, ya kamata masu sukar bai wa Badaru mukamin minista su yi biyayya ga hukuncin shugaba Tinubu.

  • Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?
  • Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Isa ya ce: “Shugaba Tinubu ya cancanci a yaba masa kan wannan mataki da ya dauka, duba da irin yadda Badaru yake da ban mamaki.”

ADVERTISEMENT

Kungiyar ta bayyana cewa a lokacin da yake rike da mukamin Gwamnan Jihar Jigawa, ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, hakan ta sa ya yi nisa a harkokin tsaro.

Da yake karin haske game da cancantar Badaru ya bayyana cewar tsohon gwamnan ba ya bukatar horon soji don gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Adamu ya jaddada cewa tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya rike mukamin a baya kuma ya taka rawar gani a wancan lokaci.

NPF ta nuna farin cikinta kan rahotannin da ke cewa Badaru ya riga ya hada tawagar kwararru domin taimaka masa wajen gudanar da ayyukansa a matsayin babban ministan tsaro.

Adamu ya tabbatar da cewa, wannan mataki na taka-tsantsan yana kara jaddada kyakkyawan hangen nesa da basirar Badaru na hada tawaga mai inganci.

An kuma bayyana fahimtar kungiyar game da manufofin tsaron kasa, inda ta lissafo muhimman abubuwa da suka hada da tabbatar da shirye-shiryen rundunar sojojin Nijeriya ta kasa, ta ruwa da ta sama, daidaita makamai da ma’aikata don bukatun tsaro, da kuma ba da fifikon jin dadin dakarun soji ta hanyar bada horo.

NPF ta bayyana muhimmancin inganta fagen tsaron kasar nan don rage dogaro da kasashen ketare da tabbatar da hadin gwiwar tsaro a shiyyar da duniya baki daya.

Adamu ya kara da cewa, “Mun yi imani cewa nada Mohammed Badaru a matsayin ministan tsaro zai kawo sauyi mai tasiri.”

A karshe kungiyar ta bayyana kudirinta na marawa Badaru baya a aikinsa na kasa tare da yin alkawarin ci gaba da yi masa addu’a don samun nasara.

Badaru
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

CMG Da Hukumar Kwallon Kafar Afirka Ta Kudu Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Yin Musaya

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.