• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Hadaka Ta ‘Yan Agaji A Abuja Ta Gudanar Da Taron Kara Wa Juna Sani

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labarai
0
Kungiyar Hadaka Ta ‘Yan Agaji A Abuja Ta Gudanar Da Taron Kara Wa Juna Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Islamic First Aid Organization” (JIFAO) da ke babban birnin tarayya Abuja ta gabatar da taron kara wa juna sani a karo na hudu.

Kungiyar hadaka na ‘yan agajin dukulallen kungiya ce wacce ta hada da kungiyoyin agaji da suka hada da na Jibwis mai shalkwata a Abuja da Jibwis da ke da shalkwata a garin Jos na Jihar Filato da Fityanul Islam of Nigeria da Jama’atu Nasrul Islam da An’nahada da Ash’shabab da kuma Initiatibe.

  • Bayan Hukuncin Kotu, Dan Takarar Sanata Na APC A Nasarawa Ya Bai Wa Magoya Bayansa Hakuri
  • Ba Zan Yi Kewar Barin Mulki Ba Saboda Kushe Ni Da ’Yan Nijeriya Ke Yi Duk Kokarina —Buhari

‘Yan agajin sun samu horo a kan abubuwa da yawa masu matukar muhimanci da suka hada da ayykan agaji shi kansa da zamantakewa da dogaro da kai da neman ilimin addini da na zamani da muhimancin hadin kan al’umma da dai sauransu.

Taron ya samu gudummuwar wasu jami’an gwamnati da kuma masu zaman kansu domin kara sanin makaman aiki. Daga cikin hukumomin da suka bayar da gudummuwar sun hada da rundunar ‘yansandan Nijeriya da hukumar kiyaye hadura da hukumar farin kaya (DSS) da hukumar shigi da fice da hukumar Cibil Defence da hukumar gyaran hali da dai sauransu.

‘Yan agaji sun tabbatar da sun samu horo a wannan haduwa mai inganci, kuma sun shaida cewa wannan karon abin ya za musu kamar shi ne na farko saboda yadda aka karantar da su.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Kungiyar Jibwis da ke Abuja karkashin jagorancin, Sheikh (Dr) Abdullahi Bala Lau ita ce ta zo ta daya a gasar fareti da aka yi a wannan hadakar, domin sun buga kafa kai ka ce sojoji ko ‘yansandan Nijeriya ne.

Shugaban JIFAO, Alh. Ahmad Adamu Jingi ya yi kira ga gwamnatin tarayya idan ta tashi daukan ma’aikata musamman a bangaren tsaro ta rika neman ‘yan agaji domin suna da kwarewa a kan harkar tsaro sosai duba da yadda ake koyar da su wannan fannin.

Daraktan Jibwis a Abuja, Alhaji Umar Isma’il wanda ya kasance kwamatan JIFAO, ya ja hankalin ‘yan agaji da su ci gaba da nuna halin da’a kamar yadda aka san su da shi, su kuma dage wajen aiki da abin da aka karantar da su domin samun nasara a wajen Allah.

Taron ya samu halartar manyan malamai da daraktoci gami da sarakuna har ma da sauran al’umma da suka hada da Draktan kungiyar Izala, Alhaji Ahmad Lau da Shugaban majalisar malamai na Abuja, Sheikh Muhammad Auwal mai Gaskiya da

Alh. Abdullahi Abdullmalik Diggi da Sarkin Bwari, Alhaji Muhammad Awwal Musa Ijakoro ll.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan AgajiAbuja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Hukuncin Kotu, Dan Takarar Sanata Na APC A Nasarawa Ya Bai Wa Magoya Bayansa Hakuri

Next Post

Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

6 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

7 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

8 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

12 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

Gwamnatin Kano Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Ga Daliban Firamare

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.