• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar ‘Yan Jarida Manema Labaru (Yobe Correspondents’ Chapel) a Jihar Yobe, ta bayyana daukar matakin raba gari da gwamnatin jihar ta hanyar kauracewa dukar dukkan labaran aikace-aikacen gwamnatin jihar.

Kungiyar, a sanarwar bayan taron gaggawa wanda ta gudanar a ranar Jumma’a, 28 ga watan Oktoba, 2022- mai dauke da sa hannun Shugabanta da Sakatare; Ahmad I. Abba da Micheal Oshomah, sun bayyana daukar matakin sakamakon cin zarafin da jami’an tsaron gidan gwamnati ke yi wa mambobinta.

  • An Yi Jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya Na Mata
  • 2022 Taron Makon Likitoci: Kebbi Ta Yi Asarar Kwararrun Likitoci 10 Cikin Shekara Guda – NMA

Kungiyar ta ce ci matakin ya zo ne sakamakon tursasawa tare da cin zarafin da jami’an tsaron gidan gwamnati ke yi wa mambobinta da rashin kallon kimar da gwamnatin jihar ke nuna wa mambobinta.

“Saboda a matsayinmu na daya daga cikin ginshikai hudu a mulkin dimukuradiyya, bangaren da ke aikin sanar da al’umma dukkan abubuwan da ke faruwa a Jihar Yobe.”

“Wanda babban abin takaici ne, ace yau sama da shekara daya amma babu dan jarida a jihar da yayi fira kai tsaye da Gwamna Mai Mala Buni, sannan wannan Kungiyar ba ta taba samun wata gayyata a hukumance daga mai magana da yawun gwamnan, Alhaji Mamman Muhammed ba, kamar yadda aka saba yi a baya.”

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Wannan ya haifar da mummunan gibi kuma yayi tasiri ga ayyukan wakilan jaridun Nijeriya daban-daban wadanda ke aiki a jihar Yobe.”

“Wanda ya toshewa dukan ‘yan jaridu masu aikin yada labaru samun duk wata damar kaiwa ga Gwamna Mai Mala Buni.”

“Saboda irin yadda wannan abin takaici ke ci gaba da gudana a karkace, kuma duk da cewa tarihi, Gwamna ya taba rike shugaban kwamitin riko a jam’iyyar APC na kasa, inda ya shafe sama da shekaru 3 ya na ganawa da manema labarai a Abuja, da sauran sassan kasar nan, amma ya kasa ya tattauna da yan jaridu a jiharsa, duk da yadda al’ummar jihar suke kewar sanin manufofin gwamnatinsa, tsare-tsare tare da ayyukan da ya aiwatar a cikin wadannan shekaru da yayi a matsayin Gwamnan jihar.”

“Wanda hakan ya jawo kungiyar ta yanke shawarar cewa ilahirin mambobinta za su daina daukar duk wani labari ko sanarwar manema labaru wanda gwamnatin jihar Yobe ta fitar har sai abin da hali yayi.”

“Haka kuma, mambobin wannan Kungiyar suna kira ga shugabannin hukumomin tsaro a jihar Yobe da su wayar da kan jami’ansu su dena cin zarafin kafafen yada labarai.”

“Sannan kuma, mambobin wannan Kungiyar ta ga cewa ya zama dole ta dauki wannan muhimmin mataki a daidai wannan gaba, domin jawo hankalin dukkan masu ruwa da tsaki da hukumomin da suka dace, saboda su dauki kwakkwaran matakin da ya dace tare da magance matsaloli da barazanar da manema labaru ke fuskanta a jihar Yobe don gyara su cikin tsanaki.”

“A karshe, muna sake nanata cewa yan jarida masu aikin yada labaru a jihar Yobe suna sanar da jama’a tare da gwamnatin jihar Yobe cewa basu dauki wannan matakin domin ra’ayin kansu ba, face kawai sai don kasancewarsu a matsayin su na daga cikin ginshikan da ke taimakon ci gaba da dorewar mulkin dimokuradiyyar kasarmu Nijeriya.”

“Har ila yau, yana da mahimmanci a lura cewa babban zabe mai zuwa yana da matukar muhimmanci a dimokuradiyyar kasarmu Nijeriya, don haka kuskure ne duk wani yunkurin yiwa kafafe yada labaru bita-da-kulli.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan JaridaGwamnatin YobeKungiyaManema LabaraiRaba GariYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Dakatar Da Mu Don Mun Nemi Mukamin Alkalin Babbar Kotun Kebbi – Wasu Alkalai

Next Post

Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.