• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
Jarida

Kungiyar ‘Yan Jarida Manema Labaru (Yobe Correspondents’ Chapel) a Jihar Yobe, ta bayyana daukar matakin raba gari da gwamnatin jihar ta hanyar kauracewa dukar dukkan labaran aikace-aikacen gwamnatin jihar.

Kungiyar, a sanarwar bayan taron gaggawa wanda ta gudanar a ranar Jumma’a, 28 ga watan Oktoba, 2022- mai dauke da sa hannun Shugabanta da Sakatare; Ahmad I. Abba da Micheal Oshomah, sun bayyana daukar matakin sakamakon cin zarafin da jami’an tsaron gidan gwamnati ke yi wa mambobinta.

  • An Yi Jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya Na Mata
  • 2022 Taron Makon Likitoci: Kebbi Ta Yi Asarar Kwararrun Likitoci 10 Cikin Shekara Guda – NMA

Kungiyar ta ce ci matakin ya zo ne sakamakon tursasawa tare da cin zarafin da jami’an tsaron gidan gwamnati ke yi wa mambobinta da rashin kallon kimar da gwamnatin jihar ke nuna wa mambobinta.

“Saboda a matsayinmu na daya daga cikin ginshikai hudu a mulkin dimukuradiyya, bangaren da ke aikin sanar da al’umma dukkan abubuwan da ke faruwa a Jihar Yobe.”

“Wanda babban abin takaici ne, ace yau sama da shekara daya amma babu dan jarida a jihar da yayi fira kai tsaye da Gwamna Mai Mala Buni, sannan wannan Kungiyar ba ta taba samun wata gayyata a hukumance daga mai magana da yawun gwamnan, Alhaji Mamman Muhammed ba, kamar yadda aka saba yi a baya.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

“Wannan ya haifar da mummunan gibi kuma yayi tasiri ga ayyukan wakilan jaridun Nijeriya daban-daban wadanda ke aiki a jihar Yobe.”

“Wanda ya toshewa dukan ‘yan jaridu masu aikin yada labaru samun duk wata damar kaiwa ga Gwamna Mai Mala Buni.”

“Saboda irin yadda wannan abin takaici ke ci gaba da gudana a karkace, kuma duk da cewa tarihi, Gwamna ya taba rike shugaban kwamitin riko a jam’iyyar APC na kasa, inda ya shafe sama da shekaru 3 ya na ganawa da manema labarai a Abuja, da sauran sassan kasar nan, amma ya kasa ya tattauna da yan jaridu a jiharsa, duk da yadda al’ummar jihar suke kewar sanin manufofin gwamnatinsa, tsare-tsare tare da ayyukan da ya aiwatar a cikin wadannan shekaru da yayi a matsayin Gwamnan jihar.”

“Wanda hakan ya jawo kungiyar ta yanke shawarar cewa ilahirin mambobinta za su daina daukar duk wani labari ko sanarwar manema labaru wanda gwamnatin jihar Yobe ta fitar har sai abin da hali yayi.”

“Haka kuma, mambobin wannan Kungiyar suna kira ga shugabannin hukumomin tsaro a jihar Yobe da su wayar da kan jami’ansu su dena cin zarafin kafafen yada labarai.”

“Sannan kuma, mambobin wannan Kungiyar ta ga cewa ya zama dole ta dauki wannan muhimmin mataki a daidai wannan gaba, domin jawo hankalin dukkan masu ruwa da tsaki da hukumomin da suka dace, saboda su dauki kwakkwaran matakin da ya dace tare da magance matsaloli da barazanar da manema labaru ke fuskanta a jihar Yobe don gyara su cikin tsanaki.”

“A karshe, muna sake nanata cewa yan jarida masu aikin yada labaru a jihar Yobe suna sanar da jama’a tare da gwamnatin jihar Yobe cewa basu dauki wannan matakin domin ra’ayin kansu ba, face kawai sai don kasancewarsu a matsayin su na daga cikin ginshikan da ke taimakon ci gaba da dorewar mulkin dimokuradiyyar kasarmu Nijeriya.”

“Har ila yau, yana da mahimmanci a lura cewa babban zabe mai zuwa yana da matukar muhimmanci a dimokuradiyyar kasarmu Nijeriya, don haka kuskure ne duk wani yunkurin yiwa kafafe yada labaru bita-da-kulli.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
Labarai

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
Next Post
Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

Haaland Yana Fama Da Jinya, Cewar Guardiola

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.