• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyin Kasashen Waje Ne Ke Daukar Nauyin Boko Haram – Buhari

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kungiyoyin Kasashen Waje Ne Ke Daukar Nauyin Boko Haram – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce wasu kungiyoyin kasa da kasa ne ke daukar nauyin ayyukan Boko Haram a kasar nan.

Buhari ya yi wannan jawabi ne a lokacin wata liyafar cin abincin shugaban kasa da gwamnatin Jihar Kano ta shirya masa yayin ziyarar aiki ta yini daya.

  • Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo
  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

“Lokacin da muka hau mulki a shekarar 2015, Boko Haram sun mamaye kananan hukumomi 13 cikin 17 na Jihar Borno, hudu ne kawai ke hannun gwamnati a lokacin.

“Sun zo ne domin hana mu ci gaba.

“Amma mun yi nasarar nunawa ‘yan Nijeriya da sauran kasashen duniya cewa muna da albarkatun kasa da yawa a yankin tafkin Chadi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

“Dole ne mu dage da addu’a kuma mu gode wa Allah, za mu yi yakin kwato kasarmu daga kungiyoyin kasa da kasa da ke kokarin ruguza Nijeriya.

“Mun yi sa’a sosai cewa wannan gwamnati ta yi abin da ya dace karkashin Gwamna Zulum na Jihar Borno, wanda ya yi matukar aiki.

“Na yi matukar farin ciki da ‘yan Nijeriya suka nuna min goyon baya. Sun gane cewar ina tare da su.

“Ina so ku tuna cewa tsakanin shekarar 1999 zuwa 2019, NNPC tana hako ganga biliyan 2.1 a rana a kan farashin dala 100 kan kowacce ganga.”

A cewarsa Nijeriya tana samun dala 100 kan kowace ganga kuma tana hako ganga miliyan 2.1 a kowace rana.

“Farashin man fetur a yau ya ragu da kusan dala 37 a kowace ganga wanda ake samar da ganga miliyan 1.5 kacal amma duk da haka mun samar da ababen more rayuwa da dama.”

“Na yi gwamna, na yi minista kuma na kasance Shugaban kasa, na yi yakin basasa.

“Dole ne mu gode wa Allah da abin da muke da shi a kasar nan a yau,” in ji shugaba Buhari.

Tun da farko Gwamna Abdullahi Ganduje ya yaba wa shugaba Buhari bisa yadda yake martaba Jihar Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBuhariDaukar NauyiKungiyoyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo

Next Post

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Fashi 2 A Delta

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

35 minutes ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

17 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Fashi 2 A Delta

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Fashi 2 A Delta

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.