• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kurar Da Ta Biyo Bayan Janye Yajin Aiki

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon ne gamayyar kungiyoyin kwadago (NLC) da kungiyar kasuwanci (TUC) suka janye shirinsu na tsunduma yajin aikin sai baba ta gani daga da suka shirya za su yi.

Wannan matakin janyewar ya zo ne, bayan wata doguwar tattaunawa tsakanin wakilan kungiyoyin da wakilan gwamnatin tarayya, yanzu dai bangarorin biyun sun cimma matsaya wadda ta kai da dakatar da tsunduma yajin aikin da kwana 30 masu zuwa.

  • Kwamishinan Benue Ya Kubuta Bayan Sace Shi Da Kwana 10
  • Takardun Karatun Tinubu Ba Na Bogi Ba Ne – Fadar Shugaban Kasa

Idan za a iya tunawa kungiyoyin sun yi shirin shiga yajin aikin ne saboda matsin rayuwa da mafi yawan ‘yan Nijeriya suke ciki, wadanda suka samo asali sakamakon cire tallafin man fetur da wasu sabbin manufofi da gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu take aiwatar da su.

Wasu daga cikin abubuwan da aka cimma akwai karin albashi na naira 35,000 da gwamnatin tarayya ta amince za ta bayar ga dukkanin ma’aikatanta, wanda za a fara daga watan Satumbar da ya gabata, kafin a samu matsaya kan sabon mafi karancin albashi wanda ake tsammanin za a mayar da shi doka.

Sannan kuma gwamnatin tarayya ta dakatar da karbar harajin kan man dizel nan da wata shida masu zuwa. Haka kuma akwai maganar motocin sufuri masu amfani da gas da ake sa ran gwamnatin za ta kawo nan ba da jimawa ba don a sami sauyi daga amfani da man fetur.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Batun biyan albashin malaman gaba da sakandire na gwamnatin tarayya da ke bin bashi, wanda shi ma an mika shi gaban ma’aikatar kwadago da ayyukan yi domin ci gaba da duba shi.

“Sanya naira biliyan 100 don sayo manyan motocin bas-bas masu amfani da man gas don saukaka wa jama’a kan hanyar zirga-zirga a duk fadin kasar nan, wanda ake sa ran za a yi a watan Nuwamba mai zuwa.

Sannan kuma an cimma yarjejeniyar cire haraji ga wasu kamfanoni da daidaikun jama’a don saukaka masu wajen hada-hadar yau da kullum.

Bugu da kari, an cimma yarjejeniyar sasantawa da kungiyar direbobi ta kasa (NURTW) tare da sanya baki a batun fara biyan naira 25,000 a duk wata daga Oktoba ga ‘yan Nijeriya mutum miliyan15, wanda ya hada da tsofaffin ma’aikata masu karbar fansho.

Akwai kuma kara fadada shirin nan na rabon taki ga manoma a duk fadin kasar nan. Haka kuma an amince da cewa su ma jihohi da kananan hukumomi za a karfafa masu gwiwa domin aiwatar da wannan karin albashi ga ma’aikatan su.

Za a samar da kudade ga matsakaita da kananan masana’antu, sannan za a mayar da hankali wajen kirkiro da ayyuka ga matasa. Sannan kuma a fito da shirin zagaya matatun man fetur din kasar nan don tantance irin gyaran da suke bukata.

Wani abu kuma shi ne, gwamnatin tarayya za ta yi amfani da takardun da kotu ta sahale ne wajen saka hannu a kan wannan yarjejeniyar fahimtar juna cikin mako daya.

Ita dai wannan yarjejeniya ta samu sanya hannun shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero da sakataren kungiyar, Emmanuel Ugboaja da shugaban kungiyar TUC, Festus Osifo da sakataren kungiyar, Nuhu A. Toro

A bangaren gwamnatin tarayya kuwa, akwai ministan kwadago, Simon Bako Lalong da karamin ministansa, Nkeiruka Onyejeocha da kuma ministan yada labarai, Alhaji Mohammed Idris.

Wannan lamari na yajin aikin kungiyar kwadago ya tayar da kura a cikin kasar nan, wanda ‘yan Nijeriya suke ta bayyana ra’ayoyinsu kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar An Hukunta Masu Zaluntar Kananan Yara Da Mata – Kwamishina Rabi Salisu

Next Post

Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

3 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

20 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

24 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.