• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kurar Da Ta Biyo Bayan Janye Yajin Aiki

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon ne gamayyar kungiyoyin kwadago (NLC) da kungiyar kasuwanci (TUC) suka janye shirinsu na tsunduma yajin aikin sai baba ta gani daga da suka shirya za su yi.

Wannan matakin janyewar ya zo ne, bayan wata doguwar tattaunawa tsakanin wakilan kungiyoyin da wakilan gwamnatin tarayya, yanzu dai bangarorin biyun sun cimma matsaya wadda ta kai da dakatar da tsunduma yajin aikin da kwana 30 masu zuwa.

  • Kwamishinan Benue Ya Kubuta Bayan Sace Shi Da Kwana 10
  • Takardun Karatun Tinubu Ba Na Bogi Ba Ne – Fadar Shugaban Kasa

Idan za a iya tunawa kungiyoyin sun yi shirin shiga yajin aikin ne saboda matsin rayuwa da mafi yawan ‘yan Nijeriya suke ciki, wadanda suka samo asali sakamakon cire tallafin man fetur da wasu sabbin manufofi da gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu take aiwatar da su.

Wasu daga cikin abubuwan da aka cimma akwai karin albashi na naira 35,000 da gwamnatin tarayya ta amince za ta bayar ga dukkanin ma’aikatanta, wanda za a fara daga watan Satumbar da ya gabata, kafin a samu matsaya kan sabon mafi karancin albashi wanda ake tsammanin za a mayar da shi doka.

Sannan kuma gwamnatin tarayya ta dakatar da karbar harajin kan man dizel nan da wata shida masu zuwa. Haka kuma akwai maganar motocin sufuri masu amfani da gas da ake sa ran gwamnatin za ta kawo nan ba da jimawa ba don a sami sauyi daga amfani da man fetur.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

Batun biyan albashin malaman gaba da sakandire na gwamnatin tarayya da ke bin bashi, wanda shi ma an mika shi gaban ma’aikatar kwadago da ayyukan yi domin ci gaba da duba shi.

“Sanya naira biliyan 100 don sayo manyan motocin bas-bas masu amfani da man gas don saukaka wa jama’a kan hanyar zirga-zirga a duk fadin kasar nan, wanda ake sa ran za a yi a watan Nuwamba mai zuwa.

Sannan kuma an cimma yarjejeniyar cire haraji ga wasu kamfanoni da daidaikun jama’a don saukaka masu wajen hada-hadar yau da kullum.

Bugu da kari, an cimma yarjejeniyar sasantawa da kungiyar direbobi ta kasa (NURTW) tare da sanya baki a batun fara biyan naira 25,000 a duk wata daga Oktoba ga ‘yan Nijeriya mutum miliyan15, wanda ya hada da tsofaffin ma’aikata masu karbar fansho.

Akwai kuma kara fadada shirin nan na rabon taki ga manoma a duk fadin kasar nan. Haka kuma an amince da cewa su ma jihohi da kananan hukumomi za a karfafa masu gwiwa domin aiwatar da wannan karin albashi ga ma’aikatan su.

Za a samar da kudade ga matsakaita da kananan masana’antu, sannan za a mayar da hankali wajen kirkiro da ayyuka ga matasa. Sannan kuma a fito da shirin zagaya matatun man fetur din kasar nan don tantance irin gyaran da suke bukata.

Wani abu kuma shi ne, gwamnatin tarayya za ta yi amfani da takardun da kotu ta sahale ne wajen saka hannu a kan wannan yarjejeniyar fahimtar juna cikin mako daya.

Ita dai wannan yarjejeniya ta samu sanya hannun shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero da sakataren kungiyar, Emmanuel Ugboaja da shugaban kungiyar TUC, Festus Osifo da sakataren kungiyar, Nuhu A. Toro

A bangaren gwamnatin tarayya kuwa, akwai ministan kwadago, Simon Bako Lalong da karamin ministansa, Nkeiruka Onyejeocha da kuma ministan yada labarai, Alhaji Mohammed Idris.

Wannan lamari na yajin aikin kungiyar kwadago ya tayar da kura a cikin kasar nan, wanda ‘yan Nijeriya suke ta bayyana ra’ayoyinsu kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar An Hukunta Masu Zaluntar Kananan Yara Da Mata – Kwamishina Rabi Salisu

Next Post

Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Related

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da É—umi-É—uminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

4 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

7 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

8 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

16 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

22 hours ago
Tattalin ArziÆ™in Nijeriya Ya BunÆ™asa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin ArziÆ™in Nijeriya Ya BunÆ™asa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

1 day ago
Next Post
Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.