Babban kwamandan Sojojin Nijeriya, Laftana Janar Olufemi Olayede ya yaba wa Shugaban kasa, Bola Tinubu na yadda ya tashi tsaye wajen ganin ya yi duk abin da ya dace ga rungnonin sojojin Nijeriya, domin su sami kwarin gwiwar sauke nauyin da aka dora masu na tabbatar da tsaro a cikin Nijeriya da kan iyakoki da suke makwabtan Nijeriya isa.
Laftana Janar Olayede ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar yayin kyan-kyashe sabbin kurattan sojoj , karo na tttyyyy da ya gudana a makarantar horar da sojojin Nijeriya da ke Zariya a Jihar Kaduna.
- Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare
- Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan
Ya ƙara da cewa babu ko shakka matakan rungumar sojojin Nijeriya da hannu biyu da kuma yadda shugaban kasa ke warware wa sojojin Nijeriya matsalolin da suke tasowa, ya ce yana matukar tasiri na nasarorin da suke samu da ya shafi tsaron kasa da kuma samun kwarin gwiwar yin fito-na-fito da ‘yan ta’adda da suke addabar Nijeriya.
shugaban sojojin ya ja kunnan sabbin kuratan da aka yaye cewa yi aiki tukuru a duk inda suka tsinci kansu a lokutan ayyukan da aka dora su a kai.
Ya yi kira a garesu na ci gaba da zama jakadu na gari a duk inda aka tura su aiki a cikin Nijeriya ko wajen Nijeriya
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp