ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

by Ibrahim Muhammad
2 years ago
Ruwa

Daya daga cikin masu neman takarar shugabancin kungiyar Musabiha ta ‘yan kasuwar kofar Ruwa da ke Kano, Abdullahi Muhammad Bala ‘Yanleman ya bayyana dalilin fitowarsa takarar da cewa saboda ganin abubuwa daban-daban da ke faruwa a kasuwar na rashin ci gaba da koma baya da take fuskanta ta sa ya fito.

Ya ce takarar da ya fito ba na yin kansa ba ne, dattawan kasuwa da matasa da sauran masu kishi da son ci gaban kasuwar ne suka ga dacewar ya ba da gudunmuwa, ganin jajircewa da yake a kan ci gaban kasuwar wajen ba da gudunmuwa sosai idan ya zama shugaba.

Alhaji ‘Yanleman ya shaida wa ‘yan jarida cewa, “Akwai matsaloli da suke damun kasuwar da yawa, musamman vangaren harkar tsaro da ta addabi kasuwar matuka, domin sai ka rufe shago ka tafi gida ka dawo da safe ka ga an valle maka, wani lokacin har fasa bango ake a shiga a kwashe mana kaya,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Ya ce yana daga cikin babban burinsa ya kyautata tsaron kasuwa da alaka da gwamnatin Jihar Kano domin a zo a rika yi musu ayyuka na ci gaba, kama daga gyaran hanyoyi da samar musu da rijiyoyin burtsatse da kuma sanya musu fitilu da za su haskaka kasuwar wajen taimaka wa harkar tsaro.

‘Yanleman ya yi nuni da cewa kungiyar tasu ta yi shugabanni da yawa tun daga kan Alhaji Mati da Alhaji Tukur, wanda daga kansa shugabanni da suka biyo baya babu abin da suka kawo wa kasuwar na ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Ya ce, “Komai ka gani ya gyaru ko ya lalace a gida daga mai gida ne. Yanzu muna duba yaya za a yi mu zo mu hada kai don gyara kasuwar, domin kasuwa tana da albarka da daraja, sannan komin dare ka zo za ka sami abin da za ka ci abinci da kai da iyalinka ballanta ma kana da abin yi, ba kamar sauran kasuwanni ba,” ya jaddada.

Ya kara da cewa kasuwar tana da tarin matasa da dimbin albarka, amma shugabanni da suka gabata da ba su da manufofi masu kyau, amma su sun shigo da manufofi masu kyau na neman wannan takara in suka yi nasara za su yi abin da za su bar tarihi ta inganta ci gaba.

Ruwa
Ibrahim Muhammad
+ postsBio
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Allah Ya Yi Wa Aminu Dantata Arzikin Da Al’umma Suka Amfana Da Shi – Abubakar

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Yadda Rahoton Bincike Ya Zargi NNPCL Da Karkatar Da Naira Biliyan 514

Yadda Rahoton Bincike Ya Zargi NNPCL Da Karkatar Da Naira Biliyan 514

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.