Akalla mutane biyu ne aka tabbatar sun mutu sakamakon barkewar cutar kwalara a wani sansani da ake ajiye Tubabbun ‘yan ta’addan Boko Haram da suka mika wuya a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.
Jami’an gwamnatin jihar Borno sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Asabar.
Sansanin Koshere na daya daga cikin wuraren da aka ware kwanan nan domin ajiye ’yan ta’addan da suka mika wuya sakamakon bukatar rage cunkoso a sansanin Hajji da aka ware tun farko domin tsugunar da tubabbun ‘yan ta’addan.
Majiyoyi a cikin sansanin sun ce adadin wadanda suka mutu a ranakun Juma’a da Asabar ya zarce 20. Amma jami’ai na sansanin sun yi fatali da adadin, inda suka ce, akwai kuskure a kirgen.
Zuwaira Gambo, kwamishiniyar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jihar, wadda ma’aikatarta ce ke kula da duk wasu kayayyakin gyara a sansanin, ta tabbatar da cewa, an samu asarar rayuka biyu sakamakon barkewar cutar kwalara da ta shafi da yawa daga cikin fursunonin sansanin na Koshere.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp