• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamandan Yaki Da ‘Yan Sara-Suka Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Zamfara

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sako Yara 74 Da Suka Sace A Zamfara Bayan Biyan Miliyan 6
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamandan kungiyar da ke yaki da ‘yan sara-suka na Jihar Zamfara, Bello Bakyasuwa, ya tsallake harin ‘yan bindiga a lokacin da yake kan hanyarsa zuwa Jihar Kaduna daga Gusau, babban birinin jihar Zamfara.

A cikin sanarwar da aka sanya wa hannu aka kuma raba wa manema labarai a yau Talata, Bakyasuwa ya bayyana cewa, ‘yan bindigar dauke da muggan makamai, sun kai masa harin a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Zariya da maraicen ranar Alhamis din da ta gabata.

  • Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 154 A Nijeriya —NCDC
  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi

Bakyasuwa wanda tsohon soja ne, ya ci gaba da cewa, “Na tsallake harin ‘yan bindigar kwanaki hudu lokacin ina kan hanyar Kaduna zuwa Funtua daga Zariya.”

Ya kara da cewa, “A yanzu haka, ina kwace a gadon asibiti, rayuwata na cikin hatsari, ina fuskantar yawan kai min hari da nake zargin wasu ‘yan bindiga ne, ke daukar nauyi. ”

Bakyasuwa ya kuma jaddada cewa, harin ya auku a kan sa ne, lokacin da yake kan hanyarsa daga Gusau zuwa Kaduna a cikin motarsa kirar Hilux, inda ya ce, ya lura da wasu motocin Hilux biyu da kuma wata motar kirar BMW na binsa a baya.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Kwamandan ya bayyana cewa, “Ganin cewa, hankali ba bai nutsu da motocin da ke bina a baya ba, sai na tsaya a wajen duba ababen hawa da ke a Yankara, inda motocin suka wuce.”

A cewarsa, “Daga nan, na ci gaba da tafiyata bayan na wuce garin Funtua da misalin karfe 8:30 na daren ranar, na lura da mota kirar Hilux da mota kirar BMW na bi na a baya, inda motar ta BMW ta shiga gabana ta kuma tilasta min tsayawa akan hanyar.”

Ya bayyana cewa,” Wadanda ke a cikin motar sai kwai suka fara bude wa motar da nake ciki wuta, inda muka shafe awanni muna yin musayar wuta da su. ”

Ya ce, “Na yi tsalle daga cikin mota ta, inda hakan ya janyo na samu raunuka a fuskata na kuma yi targade a kafata.”

Bakyasuwa ya ci gaba da cewa, ”’Yan bindigar wadanda aka yo hayarsu sun ci gaba da harbi, amma na samu nasarar tsallake wa na shiga wani daji jini na zuba daga jikina.”

Ya ce, ya ci sa a ‘yansanda sun iso wajen bayan sun ji harbin bindiga, inda suka yi gaggawar kubutar da ni suka kuma kaini asibiti.

Ya ce, “Bayan an duba ni a asibitin na kwana a kauyen da safe direbana ya zo kauyen ya sauke ni zuwa Kaduna don a duba lafiyata sosai. ”

Bakyasuwa ya bayyana cewa, motarsa ta lalace sosai biyo bayan ta sha ruwan albarusai, inda ya koka da cewa, ko a ‘yan watannin baya, wasu ‘yan bindiga sun kai wa direbansa hari a garin Gusau lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa unguwar Gwaza zuwa Gusau, inda suka kwace motarsa.

Ya yi kira ga jami’an tsaro da su kawo masa dauki, domin rayuwarsa na a cikin hatsari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HariYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 154 A Nijeriya —NCDC

Next Post

Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

7 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

8 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

10 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

11 hours ago
Next Post
Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.