ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamandan Yaki Da ‘Yan Sara-Suka Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Zamfara

by Abubakar Abba
3 years ago
Suka

Kwamandan kungiyar da ke yaki da ‘yan sara-suka na Jihar Zamfara, Bello Bakyasuwa, ya tsallake harin ‘yan bindiga a lokacin da yake kan hanyarsa zuwa Jihar Kaduna daga Gusau, babban birinin jihar Zamfara.

A cikin sanarwar da aka sanya wa hannu aka kuma raba wa manema labarai a yau Talata, Bakyasuwa ya bayyana cewa, ‘yan bindigar dauke da muggan makamai, sun kai masa harin a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Zariya da maraicen ranar Alhamis din da ta gabata.

  • Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 154 A Nijeriya —NCDC
  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi

Bakyasuwa wanda tsohon soja ne, ya ci gaba da cewa, “Na tsallake harin ‘yan bindigar kwanaki hudu lokacin ina kan hanyar Kaduna zuwa Funtua daga Zariya.”

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “A yanzu haka, ina kwace a gadon asibiti, rayuwata na cikin hatsari, ina fuskantar yawan kai min hari da nake zargin wasu ‘yan bindiga ne, ke daukar nauyi. ”

Bakyasuwa ya kuma jaddada cewa, harin ya auku a kan sa ne, lokacin da yake kan hanyarsa daga Gusau zuwa Kaduna a cikin motarsa kirar Hilux, inda ya ce, ya lura da wasu motocin Hilux biyu da kuma wata motar kirar BMW na binsa a baya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Kwamandan ya bayyana cewa, “Ganin cewa, hankali ba bai nutsu da motocin da ke bina a baya ba, sai na tsaya a wajen duba ababen hawa da ke a Yankara, inda motocin suka wuce.”

A cewarsa, “Daga nan, na ci gaba da tafiyata bayan na wuce garin Funtua da misalin karfe 8:30 na daren ranar, na lura da mota kirar Hilux da mota kirar BMW na bi na a baya, inda motar ta BMW ta shiga gabana ta kuma tilasta min tsayawa akan hanyar.”

Ya bayyana cewa,” Wadanda ke a cikin motar sai kwai suka fara bude wa motar da nake ciki wuta, inda muka shafe awanni muna yin musayar wuta da su. ”

Ya ce, “Na yi tsalle daga cikin mota ta, inda hakan ya janyo na samu raunuka a fuskata na kuma yi targade a kafata.”

Bakyasuwa ya ci gaba da cewa, ”’Yan bindigar wadanda aka yo hayarsu sun ci gaba da harbi, amma na samu nasarar tsallake wa na shiga wani daji jini na zuba daga jikina.”

Ya ce, ya ci sa a ‘yansanda sun iso wajen bayan sun ji harbin bindiga, inda suka yi gaggawar kubutar da ni suka kuma kaini asibiti.

Ya ce, “Bayan an duba ni a asibitin na kwana a kauyen da safe direbana ya zo kauyen ya sauke ni zuwa Kaduna don a duba lafiyata sosai. ”

Bakyasuwa ya bayyana cewa, motarsa ta lalace sosai biyo bayan ta sha ruwan albarusai, inda ya koka da cewa, ko a ‘yan watannin baya, wasu ‘yan bindiga sun kai wa direbansa hari a garin Gusau lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa unguwar Gwaza zuwa Gusau, inda suka kwace motarsa.

Ya yi kira ga jami’an tsaro da su kawo masa dauki, domin rayuwarsa na a cikin hatsari.

Suka
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.