ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamandan Yaki Da ‘Yan Sara-Suka Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Zamfara

by Abubakar Abba
3 years ago
Suka

Kwamandan kungiyar da ke yaki da ‘yan sara-suka na Jihar Zamfara, Bello Bakyasuwa, ya tsallake harin ‘yan bindiga a lokacin da yake kan hanyarsa zuwa Jihar Kaduna daga Gusau, babban birinin jihar Zamfara.

A cikin sanarwar da aka sanya wa hannu aka kuma raba wa manema labarai a yau Talata, Bakyasuwa ya bayyana cewa, ‘yan bindigar dauke da muggan makamai, sun kai masa harin a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Zariya da maraicen ranar Alhamis din da ta gabata.

  • Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 154 A Nijeriya —NCDC
  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi

Bakyasuwa wanda tsohon soja ne, ya ci gaba da cewa, “Na tsallake harin ‘yan bindigar kwanaki hudu lokacin ina kan hanyar Kaduna zuwa Funtua daga Zariya.”

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “A yanzu haka, ina kwace a gadon asibiti, rayuwata na cikin hatsari, ina fuskantar yawan kai min hari da nake zargin wasu ‘yan bindiga ne, ke daukar nauyi. ”

Bakyasuwa ya kuma jaddada cewa, harin ya auku a kan sa ne, lokacin da yake kan hanyarsa daga Gusau zuwa Kaduna a cikin motarsa kirar Hilux, inda ya ce, ya lura da wasu motocin Hilux biyu da kuma wata motar kirar BMW na binsa a baya.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Kwamandan ya bayyana cewa, “Ganin cewa, hankali ba bai nutsu da motocin da ke bina a baya ba, sai na tsaya a wajen duba ababen hawa da ke a Yankara, inda motocin suka wuce.”

A cewarsa, “Daga nan, na ci gaba da tafiyata bayan na wuce garin Funtua da misalin karfe 8:30 na daren ranar, na lura da mota kirar Hilux da mota kirar BMW na bi na a baya, inda motar ta BMW ta shiga gabana ta kuma tilasta min tsayawa akan hanyar.”

Ya bayyana cewa,” Wadanda ke a cikin motar sai kwai suka fara bude wa motar da nake ciki wuta, inda muka shafe awanni muna yin musayar wuta da su. ”

Ya ce, “Na yi tsalle daga cikin mota ta, inda hakan ya janyo na samu raunuka a fuskata na kuma yi targade a kafata.”

Bakyasuwa ya ci gaba da cewa, ”’Yan bindigar wadanda aka yo hayarsu sun ci gaba da harbi, amma na samu nasarar tsallake wa na shiga wani daji jini na zuba daga jikina.”

Ya ce, ya ci sa a ‘yansanda sun iso wajen bayan sun ji harbin bindiga, inda suka yi gaggawar kubutar da ni suka kuma kaini asibiti.

Ya ce, “Bayan an duba ni a asibitin na kwana a kauyen da safe direbana ya zo kauyen ya sauke ni zuwa Kaduna don a duba lafiyata sosai. ”

Bakyasuwa ya bayyana cewa, motarsa ta lalace sosai biyo bayan ta sha ruwan albarusai, inda ya koka da cewa, ko a ‘yan watannin baya, wasu ‘yan bindiga sun kai wa direbansa hari a garin Gusau lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa unguwar Gwaza zuwa Gusau, inda suka kwace motarsa.

Ya yi kira ga jami’an tsaro da su kawo masa dauki, domin rayuwarsa na a cikin hatsari.

Suka
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.