• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamishinan Cinikayya Da Zuba Jari Na Najeriya Dake Shanghai Ya Yaba Da Manufofin Kasar Sin Na Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kwamishinan Cinikayya Da Zuba Jari Na Najeriya Dake Shanghai Ya Yaba Da Manufofin Kasar Sin Na Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bikin baje-kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin karo na shida wato CIIE a birnin Shanghai dake gabashin kasar Sin, inda kwamishinan kula da harkokin cinikayya da zuba jari na yankin Asiya daga karamin ofishin jakadancin tarayyar Najeriya dake Shanghai, Ibrahim A. Ahmed ya yaba matuka da manufofin kasar Sin na fadada bude kofa ga kasashen waje, da kara shigo da kayayyaki daga kasashe daban-daban.

Wakilinmu Murtala Zhang dauke da karin bayani daga Shanghai.

  • Wakar Kidaya: Aisha Humaira Ta Nemi Al’umma Su Daina Tsangwamar Mawaki Rarara
  • Dandalin Hongqiao Na Maida Hankali Ga Kiyaye Tsarin Cinikayyar Sassa Daban Daban

Malam Ibrahim Ahmed ya ce, Najeriya na farin-cikin samun damar halartar bikin CIIE a wannan karo, ganin yadda yake samar da muhimmiyar dama ga tallata kayayyakin kasar, musamman amfanin gona da albarkatun kasa, inda ya ce:

“Tun fara bikin na bana, mutane da yawa sun zo nan don tambayar kayayyakinmu har sun yi odar wasu da dama. Mutane suna sha’awar kayayyakin Najeriya, wadanda suka bambanta da na sauran kasashen Afirka sosai. Kayayyakin Najeriya na da inganci sosai, kuma ina matukar farin-cikin ganin cewa suna samun karbuwa a wajen mutanen China.”

Sin

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Jami’in ya kara da cewa, kasar Sin ba ta taba barin kasashen Afirka a baya ba wajen samar da ci gaba, ganin yadda bikin CIIE din ke samar da wata muhimmiyar dama ga kasashen Afirka wajen raya harkokin kasuwanci, inda ya ce:

“Ya samar mana da damar mu’amala da masu zuba jari na kasar Sin, al’amarin dake da muhimmanci ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya. Don haka muna godiya ga gwamnatin kasar Sin saboda damar da ta samar mana wajen tallata kayayyakinmu a wannan bikin.”

Malam Ibrahim Ahmed ya yi karin haske cewa, Najeriya ta cimma nasarori da dama wajen halartar bikin CIIE tun daga irinsa na farko da aka yi a shekara ta 2018, kuma a bana, yana son tallata wasu muhimman nau’o’in amfanin gona, musamman gyada, da ridi, da busasshiyar citta, da sauran wasu albarkatun ma’adinai.

Sin

Da ya tabo batun burin da Najeriya take son cimmawa a wajen bikin CIIE na bana, jami’in ya ce:

“Muna fatan ganin kamfanoni da ’yan kasuwanmu kanana da matsakaita sun samu damar tallata kayayyakinsu da kyau, don kara samun ci gaban sana’o’insu.” (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaTattalin Arzikin sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Kada Kuri’a: CIIE Na Kara Kuzari Kan Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

7 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

7 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

9 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

12 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

13 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

14 hours ago
Next Post
Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

Ganawar Shugabannin Sin Da Australia Ta Share Fagen Kyautata Dangantaka

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.