• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Majalisar Dattawa Ya Nemi A Karawa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Kudi Kan Kasafin 2024

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kwamitin Majalisar Dattawa Ya Nemi A Karawa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Kudi Kan Kasafin 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin Majalisar Dattawa Mai Lura da Harkokin Yaɗa Labarai, ya nuna rashin amincewa dangane da ƙarancin kuɗaɗen da kwamitin ya ce Gwamnatin Tarayya ta ware wa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da kai, a Kasafin 2024.

Shugaban kwamitin, Sanata Kenneth Eze ne ya nuna damuwa da rashin amincewa dangane da ƙarancin kuɗaɗen, a lokacin da Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Mohammed Idris ya bayyana a gaban kwamitin, domin ya kare kasafin ma’aikatarsa, a ranar Talata, a Abuja.

  • Jamhuriyar Nijar Za Ta Fara Fitar Da Danyen Mai A Watan Janairu
  • Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna – Fauziyya

“Haba jama’a, ai waɗannan kuɗaɗe cikin cokali bai yiwuwa a ce da su kaɗai za a yi amfani har a samu biyan buƙatar yada manufofin ƙasarmu. Muddin waɗannan kuɗaɗen ne aka ware wa wannan ma’aikatar, to ba inda za mu iya cimma gaci. Ta yaya za a iya wayar da kan jama’a ta hanyar yaɗa labarai da kyawawan manufofi da waɗannan kuɗaɗe ƙalilan?

“Ma’aikatar Yaɗa Labarai fa wuri ne mai muhimmancin da wajibi ne a yi wa wurin riƙon kazar kuku, ba riƙon sakainar kashi ba. Ina magana idan har fa ana so a samu biyan buƙatar samun nasarar Ajandar Saidaita Nijeriya da mu ke magana, to dole ma’aikatar yaɗa labarai ce a sahun gaba.

“Wannan ma’aikata ce za ta kasance mai haska wa ƙasar nan fitilar kyakkyawar ɗabi’un jama’ar ta, kuma akwai wawakeken giɓi tsakanin gwamnati da jama’a, wanda wannan ma’aikatar ce tilas za ta iya cike giɓin,” inji sanatan.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

“Na duba a cikin kasafin, amma ban ga ko sisi da za a kashe a Hukumar Kula da Jaridu ba, ban ga Hukumar APCON ba, kuma ban ga kasafin wasu hukumomin da ke ƙarƙashin wannan ma’aikata ba.

“Shin gwamnati na so ta shaida mana cewa an rushe waɗannan hukumomin kenan, yadda har za su iya aiki ko ba ma’aikata a cikin su?

“Wa zai biya albashin su? Watannin baya ba da daɗewa ba fa aka naɗa wa hukumomin sabbin Manyan Daraktoci da Manyan Sakatarori.

Kenneth ya ci gaba da cewa, “Mai Girma Minista, wannan batu ne fa mai muhimmanci ga wannan kwamiti, kuma tabbas za mu duba wannan lamari.”

A nasa bayanin, Minista Idris ya shaida wa sanatocin cewa za a ƙaddamar da Shirin Cusa Ɗa’a, Kishin Ƙasa da Kyawawan Ɗabi’u (NVC) cikin 2024.

Ya ce akwai gagarimin aiki a gaban ma’aikatar sa wajen tabbatar da samun nasarar shirin cusa ɗa’a da kishin ƙasa, wanda Naira biliyan 1 da aka ware wa ma’aikatar sa, a matsayin kuɗaɗen gudanar da manyan ayyuka, ko kusa ba za su wadata ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ma'aikatar Yaɗa LabaraiMinistan yada labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Next Post

Shugaba Xi Ya Gana Da Manyan Shugabannin Kasar Vietnam

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

10 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

11 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

13 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

16 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

18 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

19 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da Manyan Shugabannin Kasar Vietnam

Shugaba Xi Ya Gana Da Manyan Shugabannin Kasar Vietnam

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.