• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani gagarumin biki, dan majalisar mai wakiltar mazabun kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde a majalisar wakilai ta kasa Honarabul Kwamoti La’ori, ya kaddamar da wani dakin taro da ya yiwa lakabi da Waziri Mbula, Chief John Eddy Manassa.

Da yake jawabi a taron, dan majalisar ya jinjinawa marigayi Waziri Mbula bisa kokarin da ya yi na hada kan jama’a, ya kuma yi addu’ar Allah ya sa ya ci gaba da zama alamar hadin kai, fahimtar juna da samar da zaman lafiya ga al’ummar yankin.

  • Kotun Koli Za Ta Saurari Shari’ar Zaben Gwamnan Adamawa A Ranar Litinin 
  • Kisan Budurwa: Gwamnatin Adamawa Za Ta Rufe Otal 70

Haka kuma ya bayyana cewa, a wani taro da aka yi a dakin taro na Prince Medan Teneke da ya gina a garin Demsa ne wasu daga mazabun suka nemi da ya gina musu ajujuwa da ya gina a Lasala, Unguwar Gwamba; Zauren jarrabawar JJ Fwa da ke gundumar Mbula, da kuma zauren John Eddy Manassa da aka kaddamar a Borrong ranar Asabar.

Don haka ya ja hankalin al’ummar mazabar da su ci gaba da tuntubarshi da maganganu masu ma’ana da kuma ra’ayoyin da za su ciyar da al’ummar mazabarsa gaba tare da tabbatar musu da cewa kunnuwansa a kowane lokaci a bude suke.

Baya ga ci gaban da aka samu wanda ya shafi mazaba a daukacin sassan mazabarsa, dan majalisar ya aiwatar da ayyukan more rayuwa daban-daban a fannin ilimi, kiwon lafiya, samar da wutar lantarki, ruwan sha da sauran muhimman sassa a kusan kashi 90% na mazabun 30 dake kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde, a karamar hukumar Demsa, mazabar Dilli ta rage bai kai ga kammala aikin ba.

Labarai Masu Nasaba

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Da itama ke jawabi kafin kaddamar da zauren taron, mataimakiyar gwamnan jihar Farfesa Kaletapwa George Farauta, ta yabawa dan majalisar bisa yadda ya dinke baraka da samar da ababen more rayuwa a mazabarsa, inda ta yi kira ga jama’a da su kula da zauren da za su rika gudanar da tarurrukan bita, liyafar aure da sauran muhimman tarukan zamantakewa a yankin.

Cikin manyan bakin da suka samu halartar taron sun hada da ‘yar majalisa mai wakiltar karamar hukumar Demsa a majalisar dokokin jihar Adamawa kuma shugaban masu rinjaye na majalisar Hon. Kate Mamuno, da dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Numan a majalisar dokokin jihar Hon. Pwamwakaino Makondo.

Shugabannin kananan hukumomin Numan, Demsa da Lamurde, Hon. Da kyar Dilli, Barr. John Tunor, Hon. Happy Maxwell, Barr Leader Teneke, Hon. Elkanah Kados, Hon. A.A Sadat, Hon. Satina, Cif Niwesa George, Dr. Ben Direi, Hon. Malena John Manassa, da ɗimbin abokan siyasa da masu ruwa da tsaki da yawa da ba za su ambatu ba.

Muhimman abubuwan da suka faru a taron sun hada da faretin ’yan wasan gargajiya daga al’ummomin masarautar Mbula. Mahayin dawakai da yawan gabatarwa a cikin wakoki da kasidu.

Murum Mbula, wanda ya karbi manya mutane a fadarsa ya samu wakilcin Cif Lawsom Gadiel, Hakimin Borrong a taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Kishin Kasa Da ‘Yan Kasa A Kasafin Kudin Nijeriya Na 2024

Next Post

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
Manyan Labarai

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

39 minutes ago
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
Manyan Labarai

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

2 hours ago
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
Labarai

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

4 hours ago
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Labarai

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

5 hours ago
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Labarai

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

6 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

9 hours ago
Next Post
Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.