• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani gagarumin biki, dan majalisar mai wakiltar mazabun kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde a majalisar wakilai ta kasa Honarabul Kwamoti La’ori, ya kaddamar da wani dakin taro da ya yiwa lakabi da Waziri Mbula, Chief John Eddy Manassa.

Da yake jawabi a taron, dan majalisar ya jinjinawa marigayi Waziri Mbula bisa kokarin da ya yi na hada kan jama’a, ya kuma yi addu’ar Allah ya sa ya ci gaba da zama alamar hadin kai, fahimtar juna da samar da zaman lafiya ga al’ummar yankin.

  • Kotun Koli Za Ta Saurari Shari’ar Zaben Gwamnan Adamawa A Ranar Litinin 
  • Kisan Budurwa: Gwamnatin Adamawa Za Ta Rufe Otal 70

Haka kuma ya bayyana cewa, a wani taro da aka yi a dakin taro na Prince Medan Teneke da ya gina a garin Demsa ne wasu daga mazabun suka nemi da ya gina musu ajujuwa da ya gina a Lasala, Unguwar Gwamba; Zauren jarrabawar JJ Fwa da ke gundumar Mbula, da kuma zauren John Eddy Manassa da aka kaddamar a Borrong ranar Asabar.

Don haka ya ja hankalin al’ummar mazabar da su ci gaba da tuntubarshi da maganganu masu ma’ana da kuma ra’ayoyin da za su ciyar da al’ummar mazabarsa gaba tare da tabbatar musu da cewa kunnuwansa a kowane lokaci a bude suke.

Baya ga ci gaban da aka samu wanda ya shafi mazaba a daukacin sassan mazabarsa, dan majalisar ya aiwatar da ayyukan more rayuwa daban-daban a fannin ilimi, kiwon lafiya, samar da wutar lantarki, ruwan sha da sauran muhimman sassa a kusan kashi 90% na mazabun 30 dake kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde, a karamar hukumar Demsa, mazabar Dilli ta rage bai kai ga kammala aikin ba.

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Da itama ke jawabi kafin kaddamar da zauren taron, mataimakiyar gwamnan jihar Farfesa Kaletapwa George Farauta, ta yabawa dan majalisar bisa yadda ya dinke baraka da samar da ababen more rayuwa a mazabarsa, inda ta yi kira ga jama’a da su kula da zauren da za su rika gudanar da tarurrukan bita, liyafar aure da sauran muhimman tarukan zamantakewa a yankin.

Cikin manyan bakin da suka samu halartar taron sun hada da ‘yar majalisa mai wakiltar karamar hukumar Demsa a majalisar dokokin jihar Adamawa kuma shugaban masu rinjaye na majalisar Hon. Kate Mamuno, da dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Numan a majalisar dokokin jihar Hon. Pwamwakaino Makondo.

Shugabannin kananan hukumomin Numan, Demsa da Lamurde, Hon. Da kyar Dilli, Barr. John Tunor, Hon. Happy Maxwell, Barr Leader Teneke, Hon. Elkanah Kados, Hon. A.A Sadat, Hon. Satina, Cif Niwesa George, Dr. Ben Direi, Hon. Malena John Manassa, da ɗimbin abokan siyasa da masu ruwa da tsaki da yawa da ba za su ambatu ba.

Muhimman abubuwan da suka faru a taron sun hada da faretin ’yan wasan gargajiya daga al’ummomin masarautar Mbula. Mahayin dawakai da yawan gabatarwa a cikin wakoki da kasidu.

Murum Mbula, wanda ya karbi manya mutane a fadarsa ya samu wakilcin Cif Lawsom Gadiel, Hakimin Borrong a taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Kishin Kasa Da ‘Yan Kasa A Kasafin Kudin Nijeriya Na 2024

Next Post

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

34 minutes ago
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida
Manyan Labarai

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

2 hours ago
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

14 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

14 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

15 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

16 hours ago
Next Post
Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.