• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani gagarumin biki, dan majalisar mai wakiltar mazabun kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde a majalisar wakilai ta kasa Honarabul Kwamoti La’ori, ya kaddamar da wani dakin taro da ya yiwa lakabi da Waziri Mbula, Chief John Eddy Manassa.

Da yake jawabi a taron, dan majalisar ya jinjinawa marigayi Waziri Mbula bisa kokarin da ya yi na hada kan jama’a, ya kuma yi addu’ar Allah ya sa ya ci gaba da zama alamar hadin kai, fahimtar juna da samar da zaman lafiya ga al’ummar yankin.

  • Kotun Koli Za Ta Saurari Shari’ar Zaben Gwamnan Adamawa A Ranar Litinin 
  • Kisan Budurwa: Gwamnatin Adamawa Za Ta Rufe Otal 70

Haka kuma ya bayyana cewa, a wani taro da aka yi a dakin taro na Prince Medan Teneke da ya gina a garin Demsa ne wasu daga mazabun suka nemi da ya gina musu ajujuwa da ya gina a Lasala, Unguwar Gwamba; Zauren jarrabawar JJ Fwa da ke gundumar Mbula, da kuma zauren John Eddy Manassa da aka kaddamar a Borrong ranar Asabar.

Don haka ya ja hankalin al’ummar mazabar da su ci gaba da tuntubarshi da maganganu masu ma’ana da kuma ra’ayoyin da za su ciyar da al’ummar mazabarsa gaba tare da tabbatar musu da cewa kunnuwansa a kowane lokaci a bude suke.

Baya ga ci gaban da aka samu wanda ya shafi mazaba a daukacin sassan mazabarsa, dan majalisar ya aiwatar da ayyukan more rayuwa daban-daban a fannin ilimi, kiwon lafiya, samar da wutar lantarki, ruwan sha da sauran muhimman sassa a kusan kashi 90% na mazabun 30 dake kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde, a karamar hukumar Demsa, mazabar Dilli ta rage bai kai ga kammala aikin ba.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

Da itama ke jawabi kafin kaddamar da zauren taron, mataimakiyar gwamnan jihar Farfesa Kaletapwa George Farauta, ta yabawa dan majalisar bisa yadda ya dinke baraka da samar da ababen more rayuwa a mazabarsa, inda ta yi kira ga jama’a da su kula da zauren da za su rika gudanar da tarurrukan bita, liyafar aure da sauran muhimman tarukan zamantakewa a yankin.

Cikin manyan bakin da suka samu halartar taron sun hada da ‘yar majalisa mai wakiltar karamar hukumar Demsa a majalisar dokokin jihar Adamawa kuma shugaban masu rinjaye na majalisar Hon. Kate Mamuno, da dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Numan a majalisar dokokin jihar Hon. Pwamwakaino Makondo.

Shugabannin kananan hukumomin Numan, Demsa da Lamurde, Hon. Da kyar Dilli, Barr. John Tunor, Hon. Happy Maxwell, Barr Leader Teneke, Hon. Elkanah Kados, Hon. A.A Sadat, Hon. Satina, Cif Niwesa George, Dr. Ben Direi, Hon. Malena John Manassa, da ɗimbin abokan siyasa da masu ruwa da tsaki da yawa da ba za su ambatu ba.

Muhimman abubuwan da suka faru a taron sun hada da faretin ’yan wasan gargajiya daga al’ummomin masarautar Mbula. Mahayin dawakai da yawan gabatarwa a cikin wakoki da kasidu.

Murum Mbula, wanda ya karbi manya mutane a fadarsa ya samu wakilcin Cif Lawsom Gadiel, Hakimin Borrong a taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Kishin Kasa Da ‘Yan Kasa A Kasafin Kudin Nijeriya Na 2024

Next Post

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

45 minutes ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

2 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

10 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

12 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

14 hours ago
Next Post
Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.