• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani gagarumin biki, dan majalisar mai wakiltar mazabun kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde a majalisar wakilai ta kasa Honarabul Kwamoti La’ori, ya kaddamar da wani dakin taro da ya yiwa lakabi da Waziri Mbula, Chief John Eddy Manassa.

Da yake jawabi a taron, dan majalisar ya jinjinawa marigayi Waziri Mbula bisa kokarin da ya yi na hada kan jama’a, ya kuma yi addu’ar Allah ya sa ya ci gaba da zama alamar hadin kai, fahimtar juna da samar da zaman lafiya ga al’ummar yankin.

  • Kotun Koli Za Ta Saurari Shari’ar Zaben Gwamnan Adamawa A Ranar Litinin 
  • Kisan Budurwa: Gwamnatin Adamawa Za Ta Rufe Otal 70

Haka kuma ya bayyana cewa, a wani taro da aka yi a dakin taro na Prince Medan Teneke da ya gina a garin Demsa ne wasu daga mazabun suka nemi da ya gina musu ajujuwa da ya gina a Lasala, Unguwar Gwamba; Zauren jarrabawar JJ Fwa da ke gundumar Mbula, da kuma zauren John Eddy Manassa da aka kaddamar a Borrong ranar Asabar.

Don haka ya ja hankalin al’ummar mazabar da su ci gaba da tuntubarshi da maganganu masu ma’ana da kuma ra’ayoyin da za su ciyar da al’ummar mazabarsa gaba tare da tabbatar musu da cewa kunnuwansa a kowane lokaci a bude suke.

Baya ga ci gaban da aka samu wanda ya shafi mazaba a daukacin sassan mazabarsa, dan majalisar ya aiwatar da ayyukan more rayuwa daban-daban a fannin ilimi, kiwon lafiya, samar da wutar lantarki, ruwan sha da sauran muhimman sassa a kusan kashi 90% na mazabun 30 dake kananan hukumomin Demsa, Numan da Lamurde, a karamar hukumar Demsa, mazabar Dilli ta rage bai kai ga kammala aikin ba.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Da itama ke jawabi kafin kaddamar da zauren taron, mataimakiyar gwamnan jihar Farfesa Kaletapwa George Farauta, ta yabawa dan majalisar bisa yadda ya dinke baraka da samar da ababen more rayuwa a mazabarsa, inda ta yi kira ga jama’a da su kula da zauren da za su rika gudanar da tarurrukan bita, liyafar aure da sauran muhimman tarukan zamantakewa a yankin.

Cikin manyan bakin da suka samu halartar taron sun hada da ‘yar majalisa mai wakiltar karamar hukumar Demsa a majalisar dokokin jihar Adamawa kuma shugaban masu rinjaye na majalisar Hon. Kate Mamuno, da dan majalisar mai wakiltar karamar hukumar Numan a majalisar dokokin jihar Hon. Pwamwakaino Makondo.

Shugabannin kananan hukumomin Numan, Demsa da Lamurde, Hon. Da kyar Dilli, Barr. John Tunor, Hon. Happy Maxwell, Barr Leader Teneke, Hon. Elkanah Kados, Hon. A.A Sadat, Hon. Satina, Cif Niwesa George, Dr. Ben Direi, Hon. Malena John Manassa, da ɗimbin abokan siyasa da masu ruwa da tsaki da yawa da ba za su ambatu ba.

Muhimman abubuwan da suka faru a taron sun hada da faretin ’yan wasan gargajiya daga al’ummomin masarautar Mbula. Mahayin dawakai da yawan gabatarwa a cikin wakoki da kasidu.

Murum Mbula, wanda ya karbi manya mutane a fadarsa ya samu wakilcin Cif Lawsom Gadiel, Hakimin Borrong a taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Kishin Kasa Da ‘Yan Kasa A Kasafin Kudin Nijeriya Na 2024

Next Post

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

41 minutes ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

3 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

15 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

17 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

19 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

22 hours ago
Next Post
Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

Bankunan Kasashen Ketare Sun Yaba Da Bunkasuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.