• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

by Abubakar Sulaiman
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayanai sun nuna cewa tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, na tattaunawa da shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kan yiwuwar komawarsa cikin jam’iyyar mai mulki.

Majiyoyi daga shalƙwatar APC a Abuja sun tabbatar da cewa tattaunawa tsakanin Kwankwaso da shugabancin jam’iyyar ta yi nisa, bayan ganawarsa da fadar shugaban ƙasa. Wasu na cikin jam’iyyar sun ce Kwankwaso ya miƙa wasiƙa zuwa shalƙwatar APC a Abuja, inda ya zayyana sharuɗɗan dawowarsa, ciki har da tabbatar da cewa gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya samu tikitin APC a zaɓen 2027.

  • Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
  • Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

Sai dai wasu jagororin APC a Kano sun bayyana cewa wasiƙar ba ta iso hannunsu ba, saboda rikicin siyasa da ya daɗe tsakanin Kwankwaso da shugabannin jam’iyyar a jihar. Duk da haka, sun ce idan ya dawo jam’iyyar, babu wanda zai hana shi shiga, tunda ya kasance ɗan siyasa mai tasiri a Kano da ma ƙasa baki ɗaya.

A makon da ya gabata, Kwankwaso ya bayyana cewa ba ya ƙin haɗa kai da APC, amma ya jaddada cewa dole a fayyace amfanin da NNPP za ta samu idan aka yi haɗin gwuiwa. A cewarsa, jam’iyyarsa na da cikakkun tsare-tsare da ‘yan takara a duk jihohi, don haka ba za ta shiga ba tare da ƙwaƙƙwarar yarjejeniya ba.

A gefe guda, manyan shugabannin APC daga Kano sun gudanar da taro a Abuja, inda suka haɗa kai wajen goyon bayan wa’adi biyu na Shugaba Bola Tinubu, tare da ƙudurin tabbatar da cewa jam’iyyar ta ƙwato mulkin Kano a zaɓen 2027.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKwankwasoNNPPTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Next Post

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

Related

Manyan Labarai

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

1 hour ago
Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

3 hours ago
Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

12 hours ago
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

15 hours ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Bankaɗo Ma’aikatan Bogi 3,488

17 hours ago
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

19 hours ago
Next Post

'Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

LABARAI MASU NASABA

Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto

Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto

September 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura

Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura

September 26, 2025

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

September 26, 2025
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

September 26, 2025
Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

September 26, 2025
Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

September 25, 2025
Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

September 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

September 25, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.