ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

by Sadiq
11 months ago
Tinubu

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya ce babu batun yin haɗin gwiwa tsakanin Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, kafin zaɓen 2027.

Yayin hira da gidan talabijin na Channels, Galadima ya zargi gwamnatin Tinubu da cin amanar Kwankwaso da NNPP a Kano, ta hanyar mara wa tsohon Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero, baya duk da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsige shi ta hanyar doka.

  • Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi
  • Dole Ne A Nace Kan Manufar Sin Daya Tak Don Kiyaye Zaman Lafiya A Mashigin Taiwan

“Ta yaya Kwankwaso zai yi abota da APC alhali suna yi mana haka a Kano? Sun kafa sarakuna biyu a gari guda; na Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin jiha. Wa ke da ikon naɗa Sarki da biyan albashinsa?” in ji Galadima.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na kare Aminy Ado Bayero ta hanyar samar masa da jami’an tsaro yayin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a wasu yankuna na Kano.

“Sun bai wa Sarkinsu (Aminu Ado Bayero) motocin ‘yansanda kusan 40 cike da jami’an Mopol, amma a wasu wurare a Kano ana kashe mutane, ana ƙwace musu wayoyi, amma ‘yansanda sun maƙale a waje ɗaya. Wannan ai abin kunya ne,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Galadima, ya tabbatar da cewa NNPP za ta taka muhimmiyar rawa wajen fitar da shugaban Nijeriya a 2027.

“Mu ne za mu yanke wanda zai zama shugaban ƙasa a 2027,” in ji shi, yana mai ƙaryata batun cewa Kwankwaso zai yi sulhu da Tinubu.

Ya ƙara da cewa: “Kar wani ya fito ya ce Kwankwaso zai shiga APC. Idan an nemi yin hakan zan sani. Kwankwaso ɗaya ne daga cikin manyan ‘yan siyasa a Nujeriya yanzu, ya ƙalubalanci APC a Kano ya kuma kayar da su.”

Rigimar sarautar Kano ta ƙara dagula siyasar jihar.

A shekarar 2014, Muhammadu Sanusi II ya zama Sarkin Kano bayan rasuwar marigayi Ado Bayero.

Amma a 2020, tsohon Gwamnan jihar Abdullahi Ganduje ya tsige shi, ya naɗa Aminu Ado Bayero.

A watan Mayun 2024, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya dawo da Sanusi II, lamarin da ya jawo Aminu Ado Bayero ya tafi kotu.

Tun daga wannan lokaci aka jibge jami’an tsaron tarayya a fadar da Aminu Ado Bayero ke zaune duk da cewa an tsige shi.

Galadima, ya ce Gwamnatin Tarayya na goyon bayan Bayero ne kawai saboda siyasa.

“Suna tunanin zai taimaka musu a 2027, amma babu wani Sarkin Kano da ya taɓa tantance wanda zai zama shugaban ƙasa,” in ji shi.

Jihar Kano ce ke da mafi yawan masu kaɗa ƙuri’a a Nijeriya.

A zaɓen 2023, ta kaɗa kusan ƙuri’u miliyan 1.7.

Kwankwaso ya fi kowa samu ƙuri’u, inda ya samu 997,279, Tinubu ya samu 517,341, Atiku Abubakar ya tashi da 131,716, yayin da Peter Obi ya samu 28,513.

Duk da cewa Kwankwaso ya zo na huɗu a zaɓen shugaban ƙasa da ƙuri’u miliyan 1.49, NNPP ta lashe zaɓe a ƙananan hukumomi 38 daga 44 a Kano, lamarin da ya nuna tasirinta a Arewa.

A halin yanzu, Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ne ke mulkin jihar, amma APC na riƙe da kujeru biyu daga cikin uku na Sanata a Kano, abin da ke nuna cewa za a kai ruwa rana a zaɓen 2027.

MASU ALAKA

inec
Manyan Labarai

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Next Post
Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

LABARAI MASU NASABA

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.