• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararru Sun Nuna Fargaba Kan Yadda Wasu Makiyaya Ke Bai Wa Dabbobinsu Magunguna Barkatai

by Abubakar Abba
5 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Kwararru Sun Nuna Fargaba Kan Yadda Wasu Makiyaya Ke Bai Wa Dabbobinsu Magunguna Barkatai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yawan amfani da magungunan kula da lafiyar dabbobi barkatai, ciki har da bangaren kiwon kifi, na ci gaba da jefa fargaba a fannin kiwon lafiyar al’ummar daukacin Nijeriya.

Masu kiwon, na bai wa dabbobinsu magunguna ne, ba tare da neman shawarar likitocin dabbobi ba, inda lamarin ke haifar da illa ga naman dabbobi da kuma kwan kajin gidan gonar da ake kiwatawa, domin kasuwanci tare kuma da illa ga madarar shanu.

  • Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Gano Tsare-Tsaren Rayuwa A Muhallin Halittu Mafi Zurfi A Teku

Magungunan warkar da dabbobin dai, na taimakawa wajen yakar kwayoyin cututtukan da ke harbin dabbobi, wanda yawan bai wa dabbobin magungunan ke jawowa su daina yin aiki a jikin dabbobin da suka kamu da kwayoyin cutar.

Kazalika, kwararru a fannin kiwon lafiyar dabbobin sun ce, yawan bai wa dabbobin magungunan, na shafar lafiyar Bil’adaman da ke cin naman dabbobin.

Daya daga cikin kwararrun, kuma Darakta a Cibyar Binken Lafiyar Dabbobi ta Kasa (NBRI) da ke Jihar Filato, Dakta DSati Ngulukun, ya shaida wa Jaridar LEADERSHIP Hausa yadda wasu masu kiwo kan dogaro a kan rade-radi da rashin yin amfani da shawarar kwararru a bangaren kula da lafiyar dabbo, musamman wajen bai wa dabbobinsu magunguna, bayan sun harbu da wasu kwayoyin cututtuka.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

“Wasu masu kiwon, suna zuwa shagunan sayar da magani ne su sayo su rika bai wa dabbobin da suka harbu da wata kwayar cuta, ba tare da yin la’akari kan adadin magungunan da ya kamata su ba su ba”, in ji Ngulukun.

Ana kuma bukatar masu kiwon su dakar da bai wa dabbonin nasu magunguna daidai da lokacin da misali, kajin gidan gona ke shirin fara yin kwai ko kuma lokacin da shanu ke shirin fara samar da madara, domin kare lafiyar mutane.

Sai dai, abin takaici shi ne, akasarin masu kiwon; ba sa kiyaye irin wadannan lokuta, wanda hakan ke shafar lafiyar mutanen da suka yi amfani da irin wadannan dabbobi.

Kazalika, yawan bai wa dabbobin magungunan barkatai don yakar wasu kwayoyin cutar da ta harbe su, na iya sanya wa ko da an bai wa dabbobin magungunan, su ki yin wani amfani a jikinsu.

Har ila yau, duk da cewa; an samar da dokoki a kan wannan matsala, sai dai, ana ci gaba da samun sakaci wajen tilasta kiyayewar yawan shayar da dabbobin magungunan barkatai, ba tare da masu kiwon sun samo shawarar Likitocin dabbobin ba.

A cewar wasu kwararru a fannin, wannan matsalar na jawo karuwar mutuwar dabbobi tare kuma da jawo asara ga masu kiwonsu.

A yanzu haka, saboda wannan batu na bai wa dabbobin magunguna, hakan ya jawo bijirewar da kwayar cutar ke yi na haifar da mutuwar dabbobi a duk shekara da yawansu ya kai kimanin miliyan 4.95, inda mafi akasari aka fi alakanta mutuwar tasu kai tsaye da kimanin miliyan 1.27, inda kwararrun suka yi gargadi da cewa, idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, nan da 2050, adadin mutuwar dabbobin zai kara rubanya zuwa miliyan 10.

Bugu da kari, Nijeriya na daga cikin kasashen da ake fuskantar irin wannan matsala, inda aka alakanta mutuwar akalla duk shekara kimanin 263,400, sakamakon rashjin jin magani da kwayoyin cutar da ke harbin dabbobin ke yi.

Wani kwararre a bangaren kula da lafiyar dabbobi, Dakta Nafiu Lawal, ya shaida wa jaridar LEADERSHIP cewa, ba a mayar da hakankali wajen wayar da kan masu kiwon dabbobin kan wannan matsala.

Dakta Nafiu, ya shawarci masu kiwon dabbobin da su rika tuntubar kwararrun likitocin dabbobi, domin samun shawarwari kan irin magungunan da ya kamata su rika bai wa dabbobin nasu, bayan sun kamu da kwayoyin cututtuka.

Sama da shekaru takwas da suka gabata, Nijeriya ta samar da tsare-tsare na kasa guda biyu a bangaren kiwo, ciki har da yadda za a dakile wannan matsala.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DabobbiFargabaMagunguna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Barkewar Cutar Lassa: Masana Sun Bayyana Hanyoyin Kare Kai

Next Post

Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

Related

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

4 hours ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

13 hours ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 days ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

7 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 week ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 weeks ago
Next Post
Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.