• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararru Sun Nuna Fargaba Kan Yadda Wasu Makiyaya Ke Bai Wa Dabbobinsu Magunguna Barkatai

by Abubakar Abba
3 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Kwararru Sun Nuna Fargaba Kan Yadda Wasu Makiyaya Ke Bai Wa Dabbobinsu Magunguna Barkatai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yawan amfani da magungunan kula da lafiyar dabbobi barkatai, ciki har da bangaren kiwon kifi, na ci gaba da jefa fargaba a fannin kiwon lafiyar al’ummar daukacin Nijeriya.

Masu kiwon, na bai wa dabbobinsu magunguna ne, ba tare da neman shawarar likitocin dabbobi ba, inda lamarin ke haifar da illa ga naman dabbobi da kuma kwan kajin gidan gonar da ake kiwatawa, domin kasuwanci tare kuma da illa ga madarar shanu.

  • Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Gano Tsare-Tsaren Rayuwa A Muhallin Halittu Mafi Zurfi A Teku

Magungunan warkar da dabbobin dai, na taimakawa wajen yakar kwayoyin cututtukan da ke harbin dabbobi, wanda yawan bai wa dabbobin magungunan ke jawowa su daina yin aiki a jikin dabbobin da suka kamu da kwayoyin cutar.

Kazalika, kwararru a fannin kiwon lafiyar dabbobin sun ce, yawan bai wa dabbobin magungunan, na shafar lafiyar Bil’adaman da ke cin naman dabbobin.

Daya daga cikin kwararrun, kuma Darakta a Cibyar Binken Lafiyar Dabbobi ta Kasa (NBRI) da ke Jihar Filato, Dakta DSati Ngulukun, ya shaida wa Jaridar LEADERSHIP Hausa yadda wasu masu kiwo kan dogaro a kan rade-radi da rashin yin amfani da shawarar kwararru a bangaren kula da lafiyar dabbo, musamman wajen bai wa dabbobinsu magunguna, bayan sun harbu da wasu kwayoyin cututtuka.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

“Wasu masu kiwon, suna zuwa shagunan sayar da magani ne su sayo su rika bai wa dabbobin da suka harbu da wata kwayar cuta, ba tare da yin la’akari kan adadin magungunan da ya kamata su ba su ba”, in ji Ngulukun.

Ana kuma bukatar masu kiwon su dakar da bai wa dabbonin nasu magunguna daidai da lokacin da misali, kajin gidan gona ke shirin fara yin kwai ko kuma lokacin da shanu ke shirin fara samar da madara, domin kare lafiyar mutane.

Sai dai, abin takaici shi ne, akasarin masu kiwon; ba sa kiyaye irin wadannan lokuta, wanda hakan ke shafar lafiyar mutanen da suka yi amfani da irin wadannan dabbobi.

Kazalika, yawan bai wa dabbobin magungunan barkatai don yakar wasu kwayoyin cutar da ta harbe su, na iya sanya wa ko da an bai wa dabbobin magungunan, su ki yin wani amfani a jikinsu.

Har ila yau, duk da cewa; an samar da dokoki a kan wannan matsala, sai dai, ana ci gaba da samun sakaci wajen tilasta kiyayewar yawan shayar da dabbobin magungunan barkatai, ba tare da masu kiwon sun samo shawarar Likitocin dabbobin ba.

A cewar wasu kwararru a fannin, wannan matsalar na jawo karuwar mutuwar dabbobi tare kuma da jawo asara ga masu kiwonsu.

A yanzu haka, saboda wannan batu na bai wa dabbobin magunguna, hakan ya jawo bijirewar da kwayar cutar ke yi na haifar da mutuwar dabbobi a duk shekara da yawansu ya kai kimanin miliyan 4.95, inda mafi akasari aka fi alakanta mutuwar tasu kai tsaye da kimanin miliyan 1.27, inda kwararrun suka yi gargadi da cewa, idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, nan da 2050, adadin mutuwar dabbobin zai kara rubanya zuwa miliyan 10.

Bugu da kari, Nijeriya na daga cikin kasashen da ake fuskantar irin wannan matsala, inda aka alakanta mutuwar akalla duk shekara kimanin 263,400, sakamakon rashjin jin magani da kwayoyin cutar da ke harbin dabbobin ke yi.

Wani kwararre a bangaren kula da lafiyar dabbobi, Dakta Nafiu Lawal, ya shaida wa jaridar LEADERSHIP cewa, ba a mayar da hakankali wajen wayar da kan masu kiwon dabbobin kan wannan matsala.

Dakta Nafiu, ya shawarci masu kiwon dabbobin da su rika tuntubar kwararrun likitocin dabbobi, domin samun shawarwari kan irin magungunan da ya kamata su rika bai wa dabbobin nasu, bayan sun kamu da kwayoyin cututtuka.

Sama da shekaru takwas da suka gabata, Nijeriya ta samar da tsare-tsare na kasa guda biyu a bangaren kiwo, ciki har da yadda za a dakile wannan matsala.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DabobbiFargabaMagunguna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Barkewar Cutar Lassa: Masana Sun Bayyana Hanyoyin Kare Kai

Next Post

Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

3 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

3 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

3 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

1 week ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

1 week ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

June 3, 2025
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.