ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararru Sun Nuna Fargaba Kan Yadda Wasu Makiyaya Ke Bai Wa Dabbobinsu Magunguna Barkatai

by Abubakar Abba
1 year ago
Fargaba

Yawan amfani da magungunan kula da lafiyar dabbobi barkatai, ciki har da bangaren kiwon kifi, na ci gaba da jefa fargaba a fannin kiwon lafiyar al’ummar daukacin Nijeriya.

Masu kiwon, na bai wa dabbobinsu magunguna ne, ba tare da neman shawarar likitocin dabbobi ba, inda lamarin ke haifar da illa ga naman dabbobi da kuma kwan kajin gidan gonar da ake kiwatawa, domin kasuwanci tare kuma da illa ga madarar shanu.

  • Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Gano Tsare-Tsaren Rayuwa A Muhallin Halittu Mafi Zurfi A Teku

Magungunan warkar da dabbobin dai, na taimakawa wajen yakar kwayoyin cututtukan da ke harbin dabbobi, wanda yawan bai wa dabbobin magungunan ke jawowa su daina yin aiki a jikin dabbobin da suka kamu da kwayoyin cutar.

ADVERTISEMENT

Kazalika, kwararru a fannin kiwon lafiyar dabbobin sun ce, yawan bai wa dabbobin magungunan, na shafar lafiyar Bil’adaman da ke cin naman dabbobin.

Daya daga cikin kwararrun, kuma Darakta a Cibyar Binken Lafiyar Dabbobi ta Kasa (NBRI) da ke Jihar Filato, Dakta DSati Ngulukun, ya shaida wa Jaridar LEADERSHIP Hausa yadda wasu masu kiwo kan dogaro a kan rade-radi da rashin yin amfani da shawarar kwararru a bangaren kula da lafiyar dabbo, musamman wajen bai wa dabbobinsu magunguna, bayan sun harbu da wasu kwayoyin cututtuka.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

“Wasu masu kiwon, suna zuwa shagunan sayar da magani ne su sayo su rika bai wa dabbobin da suka harbu da wata kwayar cuta, ba tare da yin la’akari kan adadin magungunan da ya kamata su ba su ba”, in ji Ngulukun.

Ana kuma bukatar masu kiwon su dakar da bai wa dabbonin nasu magunguna daidai da lokacin da misali, kajin gidan gona ke shirin fara yin kwai ko kuma lokacin da shanu ke shirin fara samar da madara, domin kare lafiyar mutane.

Sai dai, abin takaici shi ne, akasarin masu kiwon; ba sa kiyaye irin wadannan lokuta, wanda hakan ke shafar lafiyar mutanen da suka yi amfani da irin wadannan dabbobi.

Kazalika, yawan bai wa dabbobin magungunan barkatai don yakar wasu kwayoyin cutar da ta harbe su, na iya sanya wa ko da an bai wa dabbobin magungunan, su ki yin wani amfani a jikinsu.

Har ila yau, duk da cewa; an samar da dokoki a kan wannan matsala, sai dai, ana ci gaba da samun sakaci wajen tilasta kiyayewar yawan shayar da dabbobin magungunan barkatai, ba tare da masu kiwon sun samo shawarar Likitocin dabbobin ba.

A cewar wasu kwararru a fannin, wannan matsalar na jawo karuwar mutuwar dabbobi tare kuma da jawo asara ga masu kiwonsu.

A yanzu haka, saboda wannan batu na bai wa dabbobin magunguna, hakan ya jawo bijirewar da kwayar cutar ke yi na haifar da mutuwar dabbobi a duk shekara da yawansu ya kai kimanin miliyan 4.95, inda mafi akasari aka fi alakanta mutuwar tasu kai tsaye da kimanin miliyan 1.27, inda kwararrun suka yi gargadi da cewa, idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, nan da 2050, adadin mutuwar dabbobin zai kara rubanya zuwa miliyan 10.

Bugu da kari, Nijeriya na daga cikin kasashen da ake fuskantar irin wannan matsala, inda aka alakanta mutuwar akalla duk shekara kimanin 263,400, sakamakon rashjin jin magani da kwayoyin cutar da ke harbin dabbobin ke yi.

Wani kwararre a bangaren kula da lafiyar dabbobi, Dakta Nafiu Lawal, ya shaida wa jaridar LEADERSHIP cewa, ba a mayar da hakankali wajen wayar da kan masu kiwon dabbobin kan wannan matsala.

Dakta Nafiu, ya shawarci masu kiwon dabbobin da su rika tuntubar kwararrun likitocin dabbobi, domin samun shawarwari kan irin magungunan da ya kamata su rika bai wa dabbobin nasu, bayan sun kamu da kwayoyin cututtuka.

Sama da shekaru takwas da suka gabata, Nijeriya ta samar da tsare-tsare na kasa guda biyu a bangaren kiwo, ciki har da yadda za a dakile wannan matsala.

Fargaba
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.