ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayan Fasa-Kwauri Na Miliyan 46 A Kebbi

by Umar Faruk
4 years ago
Kwastam

Hukumar Hana Fasa-Kwauri ta Kasa (Kwastam) a Jihar Kebbi ta samu nasarar kama wasu kayan sawa na hannu na kimanin Naira miliyan 36 da kuma samar da Naira miliyan 127 a matsayin kudin shiga a watan Nuwamba.

Shugaban Hukumar Kwastam, Kwanturola Joseph Attah ne, ya bayyana hakan ga manema labarai a Birnin Kebbi, yayin da yake baje kolin kayayyakin da hukumar ta kama a watan da ya gabata.

  • Kyawawan Halaye 2: Wasu Annabawa Da Sauran Bayin Allah Da Suka Yi Magana A Tsummar Jego
  • Shugaban Kasar Sin Ya Yi Shawarwari Da Manyan Shugabannin Kasar Saudiyya Da Kuma Gana Da Shugabannin Wasu Kasashen Larabawa Bi da Bi

Da yake ba da cikakken bayani kan ayyukan rundunar, Attah ya ce, rundunar ta samu kudi miliyan dari da ashirin da bakwai, da dubu dari takwas da talatin da tara, da naira dari uku da casa’in (127,839,390.75) a matsayin kudaden shiga daga shigo da kayan fasa-kwauri a kan hanyar iyakar Kamba da ke Jamhuriyar Nijar daga Jihar kebbi.

ADVERTISEMENT

A bangaren yaki da fasa-kwauri, ya bayyana cewa, a yayin da ake ci gaba da sintiri a fadin Jihar Kebbi, rundunar ta samu nasarar kame wasu kayayyaki da suka hada da dila 303 da buhu 94 na tufafin gwanjo guda 94, mota kirar BMW guda daya, lita mai 2,375 a cikin jarkoki da kuma buhunan shinkafa 58 na kasar waje mai nauyin kilo 50 kowanne; da sauran wadanda kudin harajinsu ya kai miliyan arba’in da shida, da dubu dari bakwai da shida, da naira dari bakwai da casa’in da biyar (46,706,795.00).

Haka kuma, Kwanturola Joseph Attah, ya ba da tabbacin cewa jami’ansa a shirye suke su dakile ayyukan masu fasa-kwauri saboda rundunar tana da kayan aikin da suka dace don gudanar da aikin a kowane lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Daga bayanan da muka samu, an samu karuwar kayan fasa-kwauri a cikin watanni biyu da suka gabata.”

“Idan za a tuna cewa an kuma kama dilar gwanjo 139 a watan Oktoba.

“Masu fasa-kwaurin suna biyan bukatun mutane masu kauri irin su cardigans a wannan lokacin na sanyi don safarar wadannan tufafin da aka yi amfani da su, ba tare da la’akari da tasirin kiwon lafiya ba har zuwa karshen amfani da su.

“Ba mu san daga ina kayan suka fito ba ko kuma na karshe masu amfani da tufafin, yanayin lafiyarsu da sauransu.

“Don guje wa shakku, tufafin hannu na biyu sun fado a karkashin jadawalin kasuwanci na (CET) 2022-2026, wanda aka haramta shigo da shi a kasan lafiya. Batun fasa kwaurinta ya ci karo da sashe na 46 na dokar hukumar kwastam (CEMA) CAP C. 45 LFN, 2004 (kamar wadda aka yi wa kwaskwarima).

“Hakkin hukumar kwastam ne ta tabbatar da cewa ba a bar wani abu da zai iya cutar da mutanen kasa ba. Mun kuduri aniyar yin hakan,” in ji shi.

Hukumar ta yaba da tallafin da hukumar ke bayarwa ta hanyar samar da dabaru kuma ta kuduri aniyar tunkarar masu fasa-kwauri a jahohin kasar nan.

Hukumar ta CAC ta yi kira ga duk masu hannu da shuni da su tallafa wa rundunar ofishin Kwastam na Jihar Kebbi ta hanyar samar da bayanai masu inganci don samun nasarorin gudanar da ayyukan dakile fasa-kwauri.

Kwastam
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
An Mikawa Kamfanin China Eastern Jirgin Sama Kiran C919 Na Farko Da Kasar Sin Ta Kera Da Kanta

An Mikawa Kamfanin China Eastern Jirgin Sama Kiran C919 Na Farko Da Kasar Sin Ta Kera Da Kanta

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.