ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Yi Shawarwari Da Manyan Shugabannin Kasar Saudiyya Da Kuma Gana Da Shugabannin Wasu Kasashen Larabawa Bi da Bi

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da sarkin masarautar Saudiyya, Salman bin Abdul Aziz Al Saud a fadarsa dake birnin Riyadh a ran 8 ga wata da yamma, agogon wuri.

Xi ya ce, kasarsa ta mayar da Saudiyya a matsayin wata muhimmiyar kasa dake taka rawar gani a harkokin duniya, inda take fatan kara mu’amalar manyan tsare-tsare tare da Saudiyya, da zurfafa hadin-gwiwa a bangarori daban-daban, a wani kokari na kiyaye moriyarsu, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

  • Rashin Tsoma Baki Ya Sa Kasar Sin Ke Samun Karin Abokai

A nasa bangaren, sarki Salman ya yi marhabin lale da zuwan shugaba Xi, inda a cewarsa, yana matukar maida hankali kan raya dangantaka tare da kasar Sin, da kuma bayyana fatansa na samar da ci gaban huldodin kasashen biyu, bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkanin fannoni.

ADVERTISEMENT

Shugabannin biyu sun kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar kulla dangantakar abota bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkanin fannoni, tsakanin Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin da kasar Saudiyya, inda suka amince cewa, za su gana a kasashensu a kowace shekara.

A dai wannan rana, shugaba Xi ya yi shawarwari tare da yariman masarautar Saudiyya, kana firaministan kasar Muhammad bin Salman bin Abdel Aziz Al Saud, inda suka yarda cewa, za su daga matsayin shugabancin kwamitin hadin-gwiwar manyan jami’an kasashen biyu, zuwa matsayin firaminista.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Shugabannin biyu sun kuma halarci bikin mika wa juna takardun yarjeniyoyin hadin-gwiwar kasashensu, a fannonin da suka shafi raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, da aikin shari’a, da ilimi, da makamashin hydrogen, da zuba jari, da gidajen kwana da sauransu.

Bayan shawarwarin, shugaba Xi ya halarci bikin maraba da yariman Muhammad ya shirya masa, a madadin sarkin Salman bin Abdul Aziz Al Saud.

Sannan a wannan rana da yamma, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya kuma gana da takwaransa na kasar Masar, Abdel Fattah al Sisi a Riyadh, babban birnin kasar Saudiyya.

Yayin ganawar, Xi ya ce, bisa halin da ake ciki yanzu a duk duniya, da ma shiyyoyi daban-daban na fuskantar manyan sauye-sauye, yana da muhimmanci a raya huldodin Sin da Masar bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkan fannoi. Ya ce ya dace kasashen biyu su yi kokari tare, don neman cimma burin gina al’ummominsu masu kyakkyawar makoma ta bai daya, ta yadda za’a kara samar da sabon ci gaba, ga dangantakarsu bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkan fannoni.

A nasa bangaren, shugaba Sisi ya ce, ya zo kasar Sin don halartar bikin bude gasar wasannin Olympics ta lokacin hunturu da aka yi a watan Fabrairun bana a Beijing, inda ya yi shawarwari masu gamsarwa tare da shugaba Xi. Ya ce, ya ziyarci kasar Sin a wancan lokacin ne don goyon bayan kasar, da karfafa dangantaka tare da kasar. Sisi yana da yakinin cewa, a sabon wa’adin aikin shugaba Xi, dangantakar kasashen biyu za ta samu karin ci gaba, kana, kwalliya za ta biya kudin sabulu, wajen karfafa hadin-gwiwarsu a bangaren shawarar “ziri daya da hanya daya”.

Bugu da kari, da safiyar yau 9 ga wata ne, bi da bi shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwarorinsa na kasar Tunisiya Kais Saied da na kasar Mauritaniya Mohamed Ould Ghazouani da na kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh da na kasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamud da na Comoros Azali Assoumani da firaministan kasar Iraki Mohammed Shia al-Sudani da sarki Tamim Bin Hamad Al Thani na masarautar Qatar a birnin Riyadh, fadar mulkin kasar Saudiyya. (Murtala Zhang, Ibrahim Yaya)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Gasar Cin Kofin Duniya: Croatia Ta Kora Brazil Gida

Gasar Cin Kofin Duniya: Croatia Ta Kora Brazil Gida

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.