• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Mutane 4 Kan Zargin Fasa-Kwauri, Sun Tara Sama Da N179m A Katsina 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kwastam Ta Kama Mutane 4 Kan Zargin Fasa-Kwauri, Sun Tara Sama Da N179m A Katsina 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an Hukumar Hana Fasa-Kwauri ta Kasa (NCS), a Jihar Katsina sun kama wasu mutane hudu da ake zargi yin safarar kayayyaki a jihar.

Duk da cewa an bayar da belin wadanda ake zargin har sai an kammala bincike, hukumar kwastam ta Jihar Katsina ta danganta nasarorin da aka samu a cikin wannan lokaci da ake bitar da su da jajircewa da jami’an rundunar suka yi tare da hadin gwiwar saura hukumomin tsaro.

  • ‘Yan Daba Sun Afkawa Gidan Wani Mai Goyan Bayan Atiku Sun Masa Ta’addanci A Jihar Ribas
  • Hukumar Kwastam Ta Kwace Litar Man Fetur 85,300 A Jihar Ogun

Kwanturolan hukumar kwastam mai kula da Jihar Katsina, Dalha Wada Chedi ne, ya bayyana hakan a ranar Talata a hedikwatar rundunar da ke Katsina yayin taron manema labarai na wata-wata da rundunar ta gudanar kan ayyukan da ta ke yi.

Chedi a yayin da yake baje kolin wasu kayayyakin da rundunar ta kama, ya yi kira ga al’ummar jihar da ‘yan kasuwa da su yi amfani da damar da aka sake bude kan iyakar Jibiya domin gudanar da harkokinsu na kan iyaka.

Ya kara da cewa har yanzu sauran kan iyakokin na rufe, don haka wucewa ko yunkurin wuce gona da iri ya sabawa doka saboda ingantacciyar manufar Gwamnatin Tarayya ta rufe iyakokin.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

“Yayin da muke dosar shekara mai kamawa, rundunar za ta ci gaba da samar da dabarun tattara bayanan sirri masu karfi a kan tsaron kan iyaka da tabbatar da ingantaccen yanayi na hada-hadar kasuwanci tare da inganta hanyoyinmu na yaki da fasa-kwauri domin murkushe abubuwan da aka yi fasakwaurin wanda ke haifar da babbar barazana ga tattalin arziki da tsaron kasar nan,” in ji shi.

A cewar Kwanturolan na Kwastam, rundunar ta samu N179,206,288.33 a hannun wadanda suka shiga hannu.

Ya nuna karin Naira miliyan 58 daga miliyan 121,800,478.00 da aka tara a watan Oktoban 2022, wanda ke nuna karin kashi 47% na kudaden shiga da aka tara.

A lokacin da ake bitar rundunar, ya bayyana cewa, motocin da aka kama masu fasa-kwaurinsu da hanyoyin jigilar kayayyaki kamar buhunan shinkafa 239 na kasar waje mai nauyin kilogiram 50 kowanne da kudin harajin N7,098,300.00, buhu biyu na shinkafar kasar waje mai nauyin kilogiram 25, sai katan-katan guda 821 na taliyar kasar waje.

Ya ce hukumar za ta ci gaba da yaki da fasa-kwaurin kayayyaki daga kasashen ketare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fasa KwauriKatsinaKwastam
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Daba Sun Afkawa Gidan Wani Mai Goyan Bayan Atiku Sun Masa Ta’addanci A Jihar Ribas

Next Post

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

Related

Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 
Manyan Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

2 hours ago
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

4 hours ago
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000
Manyan Labarai

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

6 hours ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

7 hours ago
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano
Manyan Labarai

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

9 hours ago
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi
Manyan Labarai

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

13 hours ago
Next Post
Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

August 28, 2025
Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

August 28, 2025
Jimillar Kudaden Jigilar Kayayyaki a Watanni 7 Na Farkon Bana a Sin Ta Zarce Rmb Yuan Tiriliyan 200

Jimillar Kudaden Jigilar Kayayyaki a Watanni 7 Na Farkon Bana a Sin Ta Zarce Rmb Yuan Tiriliyan 200

August 28, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

August 28, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

August 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

August 28, 2025
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

August 28, 2025
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

August 28, 2025
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

August 28, 2025
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

August 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.