• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Mutane 4 Kan Zargin Fasa-Kwauri, Sun Tara Sama Da N179m A Katsina 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kwastam Ta Kama Mutane 4 Kan Zargin Fasa-Kwauri, Sun Tara Sama Da N179m A Katsina 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an Hukumar Hana Fasa-Kwauri ta Kasa (NCS), a Jihar Katsina sun kama wasu mutane hudu da ake zargi yin safarar kayayyaki a jihar.

Duk da cewa an bayar da belin wadanda ake zargin har sai an kammala bincike, hukumar kwastam ta Jihar Katsina ta danganta nasarorin da aka samu a cikin wannan lokaci da ake bitar da su da jajircewa da jami’an rundunar suka yi tare da hadin gwiwar saura hukumomin tsaro.

  • ‘Yan Daba Sun Afkawa Gidan Wani Mai Goyan Bayan Atiku Sun Masa Ta’addanci A Jihar Ribas
  • Hukumar Kwastam Ta Kwace Litar Man Fetur 85,300 A Jihar Ogun

Kwanturolan hukumar kwastam mai kula da Jihar Katsina, Dalha Wada Chedi ne, ya bayyana hakan a ranar Talata a hedikwatar rundunar da ke Katsina yayin taron manema labarai na wata-wata da rundunar ta gudanar kan ayyukan da ta ke yi.

Chedi a yayin da yake baje kolin wasu kayayyakin da rundunar ta kama, ya yi kira ga al’ummar jihar da ‘yan kasuwa da su yi amfani da damar da aka sake bude kan iyakar Jibiya domin gudanar da harkokinsu na kan iyaka.

Ya kara da cewa har yanzu sauran kan iyakokin na rufe, don haka wucewa ko yunkurin wuce gona da iri ya sabawa doka saboda ingantacciyar manufar Gwamnatin Tarayya ta rufe iyakokin.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

“Yayin da muke dosar shekara mai kamawa, rundunar za ta ci gaba da samar da dabarun tattara bayanan sirri masu karfi a kan tsaron kan iyaka da tabbatar da ingantaccen yanayi na hada-hadar kasuwanci tare da inganta hanyoyinmu na yaki da fasa-kwauri domin murkushe abubuwan da aka yi fasakwaurin wanda ke haifar da babbar barazana ga tattalin arziki da tsaron kasar nan,” in ji shi.

A cewar Kwanturolan na Kwastam, rundunar ta samu N179,206,288.33 a hannun wadanda suka shiga hannu.

Ya nuna karin Naira miliyan 58 daga miliyan 121,800,478.00 da aka tara a watan Oktoban 2022, wanda ke nuna karin kashi 47% na kudaden shiga da aka tara.

A lokacin da ake bitar rundunar, ya bayyana cewa, motocin da aka kama masu fasa-kwaurinsu da hanyoyin jigilar kayayyaki kamar buhunan shinkafa 239 na kasar waje mai nauyin kilogiram 50 kowanne da kudin harajin N7,098,300.00, buhu biyu na shinkafar kasar waje mai nauyin kilogiram 25, sai katan-katan guda 821 na taliyar kasar waje.

Ya ce hukumar za ta ci gaba da yaki da fasa-kwaurin kayayyaki daga kasashen ketare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fasa KwauriKatsinaKwastam
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Daba Sun Afkawa Gidan Wani Mai Goyan Bayan Atiku Sun Masa Ta’addanci A Jihar Ribas

Next Post

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

3 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

3 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

14 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

15 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

1 day ago
Next Post
Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Fasa-Kwauri

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.