• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Mutane 4 Kan Zargin Fasa-Kwauri, Sun Tara Sama Da N179m A Katsina 

by Sadiq
3 years ago
Fasa-Kwauri

Jami’an Hukumar Hana Fasa-Kwauri ta Kasa (NCS), a Jihar Katsina sun kama wasu mutane hudu da ake zargi yin safarar kayayyaki a jihar.

Duk da cewa an bayar da belin wadanda ake zargin har sai an kammala bincike, hukumar kwastam ta Jihar Katsina ta danganta nasarorin da aka samu a cikin wannan lokaci da ake bitar da su da jajircewa da jami’an rundunar suka yi tare da hadin gwiwar saura hukumomin tsaro.

  • ‘Yan Daba Sun Afkawa Gidan Wani Mai Goyan Bayan Atiku Sun Masa Ta’addanci A Jihar Ribas
  • Hukumar Kwastam Ta Kwace Litar Man Fetur 85,300 A Jihar Ogun

Kwanturolan hukumar kwastam mai kula da Jihar Katsina, Dalha Wada Chedi ne, ya bayyana hakan a ranar Talata a hedikwatar rundunar da ke Katsina yayin taron manema labarai na wata-wata da rundunar ta gudanar kan ayyukan da ta ke yi.

Chedi a yayin da yake baje kolin wasu kayayyakin da rundunar ta kama, ya yi kira ga al’ummar jihar da ‘yan kasuwa da su yi amfani da damar da aka sake bude kan iyakar Jibiya domin gudanar da harkokinsu na kan iyaka.

Ya kara da cewa har yanzu sauran kan iyakokin na rufe, don haka wucewa ko yunkurin wuce gona da iri ya sabawa doka saboda ingantacciyar manufar Gwamnatin Tarayya ta rufe iyakokin.

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

“Yayin da muke dosar shekara mai kamawa, rundunar za ta ci gaba da samar da dabarun tattara bayanan sirri masu karfi a kan tsaron kan iyaka da tabbatar da ingantaccen yanayi na hada-hadar kasuwanci tare da inganta hanyoyinmu na yaki da fasa-kwauri domin murkushe abubuwan da aka yi fasakwaurin wanda ke haifar da babbar barazana ga tattalin arziki da tsaron kasar nan,” in ji shi.

A cewar Kwanturolan na Kwastam, rundunar ta samu N179,206,288.33 a hannun wadanda suka shiga hannu.

Ya nuna karin Naira miliyan 58 daga miliyan 121,800,478.00 da aka tara a watan Oktoban 2022, wanda ke nuna karin kashi 47% na kudaden shiga da aka tara.

A lokacin da ake bitar rundunar, ya bayyana cewa, motocin da aka kama masu fasa-kwaurinsu da hanyoyin jigilar kayayyaki kamar buhunan shinkafa 239 na kasar waje mai nauyin kilogiram 50 kowanne da kudin harajin N7,098,300.00, buhu biyu na shinkafar kasar waje mai nauyin kilogiram 25, sai katan-katan guda 821 na taliyar kasar waje.

Ya ce hukumar za ta ci gaba da yaki da fasa-kwaurin kayayyaki daga kasashen ketare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Next Post
Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.