ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Mutane 4 Kan Zargin Fasa-Kwauri, Sun Tara Sama Da N179m A Katsina 

by Sadiq
4 years ago
Fasa-Kwauri

Jami’an Hukumar Hana Fasa-Kwauri ta Kasa (NCS), a Jihar Katsina sun kama wasu mutane hudu da ake zargi yin safarar kayayyaki a jihar.

Duk da cewa an bayar da belin wadanda ake zargin har sai an kammala bincike, hukumar kwastam ta Jihar Katsina ta danganta nasarorin da aka samu a cikin wannan lokaci da ake bitar da su da jajircewa da jami’an rundunar suka yi tare da hadin gwiwar saura hukumomin tsaro.

  • ‘Yan Daba Sun Afkawa Gidan Wani Mai Goyan Bayan Atiku Sun Masa Ta’addanci A Jihar Ribas
  • Hukumar Kwastam Ta Kwace Litar Man Fetur 85,300 A Jihar Ogun

Kwanturolan hukumar kwastam mai kula da Jihar Katsina, Dalha Wada Chedi ne, ya bayyana hakan a ranar Talata a hedikwatar rundunar da ke Katsina yayin taron manema labarai na wata-wata da rundunar ta gudanar kan ayyukan da ta ke yi.

ADVERTISEMENT

Chedi a yayin da yake baje kolin wasu kayayyakin da rundunar ta kama, ya yi kira ga al’ummar jihar da ‘yan kasuwa da su yi amfani da damar da aka sake bude kan iyakar Jibiya domin gudanar da harkokinsu na kan iyaka.

Ya kara da cewa har yanzu sauran kan iyakokin na rufe, don haka wucewa ko yunkurin wuce gona da iri ya sabawa doka saboda ingantacciyar manufar Gwamnatin Tarayya ta rufe iyakokin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

“Yayin da muke dosar shekara mai kamawa, rundunar za ta ci gaba da samar da dabarun tattara bayanan sirri masu karfi a kan tsaron kan iyaka da tabbatar da ingantaccen yanayi na hada-hadar kasuwanci tare da inganta hanyoyinmu na yaki da fasa-kwauri domin murkushe abubuwan da aka yi fasakwaurin wanda ke haifar da babbar barazana ga tattalin arziki da tsaron kasar nan,” in ji shi.

A cewar Kwanturolan na Kwastam, rundunar ta samu N179,206,288.33 a hannun wadanda suka shiga hannu.

Ya nuna karin Naira miliyan 58 daga miliyan 121,800,478.00 da aka tara a watan Oktoban 2022, wanda ke nuna karin kashi 47% na kudaden shiga da aka tara.

A lokacin da ake bitar rundunar, ya bayyana cewa, motocin da aka kama masu fasa-kwaurinsu da hanyoyin jigilar kayayyaki kamar buhunan shinkafa 239 na kasar waje mai nauyin kilogiram 50 kowanne da kudin harajin N7,098,300.00, buhu biyu na shinkafar kasar waje mai nauyin kilogiram 25, sai katan-katan guda 821 na taliyar kasar waje.

Ya ce hukumar za ta ci gaba da yaki da fasa-kwaurin kayayyaki daga kasashen ketare.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci Emefiele Kan Takaita Cire Kudade 

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.