• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, a yayin da al’ummar musulmi a sassan duniya suka yi shagulgulan babbar sallah, wani abu da ya faru a Turai ya bata yanayin bikin, inda bisa amincewar ’yan sandan wurin, an sake samun wani da ya kona Alkur’ani mai tsarki a wajen wani masallacin da ke birnin Stockholm, babban birnin kasar Sweden.

Bayan aukuwar lamarin, firaministan kasar ta Sweden Ulf Kristersson ya bayyana cewa, duk da cewa lamarin bai dace ba, amma ba a karya doka ba. Shi kuma kakakin majalisar harkokin wajen Amurka Matthew Miller ya furta cewa, Amurka na goyon bayan ’yancin jama’a na fadin albarkacin baki, kasancewarsa wani bangare na dimokuradiyya. Sai kuma babban sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg da ya ce, wannan na daga cikin ’yancin jama’a na fadi albarkacin bakinsu. Lallai irin matsayin da kasashen yammacin duniya suka dauka ya jawo suka daga gamayyar kasa da kasa, musamman ma kasashen musulmi.

  • Ziyarar Firaministan Kasar Tsibiran Solomon A Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana Ga Kasar

Dangane da aukuwar lamarin, daga ranar 11 zuwa 12 ga wata, an gudanar da muhawara ta gaggawa a gun taron majalisar kula da hakkin dan Adam ta MDD karo na 53, inda zaunannen wakilin kasar Sin a ofishin MDD da ke Geneva ya yi Allah wadai da aukuwar lamarin da kakkausar murya, ya ce, a kullum kasar Sin na ganin cewa, ya kamata a yayata akidar martaba juna, da tafiya tare da dukkanin sassa, da koyi da juna tsakanin mabanbantan al’ummu, kuma tana tsayawa tsayin daka a kan kin yarda da nuna kyamar musulunci.

Lamarin da ya faru a kasar Sweden ba shi ne karo na farko ba. A cikin ’yan shekarun baya, a yayin da ake ta kara samun rikici a tsakanin sassan duniya, wasu ’yan siyasar kasashen yammacin duniya na ta kara tunzura fito na fito tsakanin al’ummu da wayewar kansu. Idan ba a manta ba, mujallar Charlie Hebdo ta Faransa ta sha wallafa zanen barkwanci da suka tada sabani a tsakanin addinai da kabilu daban daban. Tun daga watan Agustan shekarar 2020, sau da dama, wasu tsirarrun ’yan siyasar Turai sun kona Alkur’ani mai tsarki a fili. A watan Janairun shekarar 2017, gwamnatin kasar Amurka ta kaddamar da dokar kayyade shigar da al’ummar kasashen musulmi kasar, matakin da ya sa ta zama kasa daya tilo a duniya da ta sanya haramci kan rukunin al’ummar musulmi. Duk wadannan lamura sun tunzura kiyayya a tsakanin mabambantan al’ummu, tare da tsananta rashin fahimtar juna a tsakanin kabilu daban daban, kuma ainihin dalilin da ya sa haka shi ne yadda kasashen yammacin duniya ke nuna bambanci ga irin al’ummun da ba nasu ba, wadanda a ganinsu, wayewar kai na yammacin duniya ya fi na sauran sassan duniya.

Kasar Sin a nata bangaren, tana ganin cewa, duk da bambance bambance da ke tsakanin wayewar kai iri iri, amma babu wani da ya fi wani na daban, don haka ma, kullum take kira da a kiyaye kasancewar mabambantan wayewar kai, tare da sa kaimin yin musaya a tsakaninsu. Kuma hakan ya faru ne sakamakon yadda kasar Sin ta kasance kasar da ke da kabilu da dama tun fil azal, wadanda suka yi ta zaman cude-ni-in-cude-ka a tsawon tarihi na kasar, a yayin da kuma suka yi ta yin musayar wayewar kansu tare da samun ci gaba tare. Baya ga haka kuma, addinai da dama, ciki har da addinin Buddah, da Musulunci da Kirisita duk sun shigo nan kasar har sun samu bunkasa sun zama muhimman bangarori na wayewar kan kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Sabo da irin wannan akidar martaba mabambantan wayewar kai da kasar Sin ke da shi, a watan Maris na wannan shekara, kasar ta gabatar da shawarar bunkasa wayewar kai tsakanin al’ummun kasa da kasa, inda ta yi kira da a aiwatar da manufofin daidaito, da koyi da juna, da tattaunawa, da tafiya tare tsakanin dukkanin wayewar kan al’ummun duniya.

Wayewar kan musulunci ta bayar da gagarumar gudummawa ga ci gaban duniya, kuma an sha yin musaya a tsakanin wayewar kan al’ummar kasar Sin da na musulunci, matakin da ya zama misali na yin musaya a tsakanin wayewar kai daban daban. Kawo yanzu, kasar Sin da kasashen musulmi sun gudanar da taron kara wa juna sani game da wayewar kan juna har sau hudu. A ranar 15 ga watan Maris na shekarar 2022 kuma, kasar Sin ta sa kaimi ga taron MDD ya zartas da kudurin tsai da ranar 15 ga watan Maris na kowace shekara a matsayin “ranar duniya ta adawa da kyamar musulunci”.

Kasancewar bambance-bambance dake tsakanin wayewar kai daban daban, shi ya sa suke yin musaya a tsakaninsu, kuma sabo da irin musaya ne, ake samun ci gaba na bai daya, don haka muke cewa kyan wayewar kai na cikin bambance-banbancen dake akwai tsakaninsu. Muna fatan kasa da kasa za su hada hannu su yayata shawarar bunkasa wayewar kai tsakanin al’ummun kasa da kasa, don kiyaye mabambantan wayewar kan al’ummmun duniya. A sa’i daya kuma, muna fatan wasu kasashen yamma za su dauki matakai, don daidaita ainihin matsalolin nuna bambanci, kuma su karfafa fahimtar addinai da wayewar kai da ba irin nasu ba. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kulla Dangantakar Diplomasiyya Tare Da Sin, Daya Ne Daga Cikin Kudurori Mafi Dacewa Da Kasar Tsibiran Solomon Ta Tsai Da A Tarihi

Next Post

Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

4 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

5 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

6 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

7 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

8 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

18 hours ago
Next Post
Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.