• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, a yayin da al’ummar musulmi a sassan duniya suka yi shagulgulan babbar sallah, wani abu da ya faru a Turai ya bata yanayin bikin, inda bisa amincewar ’yan sandan wurin, an sake samun wani da ya kona Alkur’ani mai tsarki a wajen wani masallacin da ke birnin Stockholm, babban birnin kasar Sweden.

Bayan aukuwar lamarin, firaministan kasar ta Sweden Ulf Kristersson ya bayyana cewa, duk da cewa lamarin bai dace ba, amma ba a karya doka ba. Shi kuma kakakin majalisar harkokin wajen Amurka Matthew Miller ya furta cewa, Amurka na goyon bayan ’yancin jama’a na fadin albarkacin baki, kasancewarsa wani bangare na dimokuradiyya. Sai kuma babban sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg da ya ce, wannan na daga cikin ’yancin jama’a na fadi albarkacin bakinsu. Lallai irin matsayin da kasashen yammacin duniya suka dauka ya jawo suka daga gamayyar kasa da kasa, musamman ma kasashen musulmi.

  • Ziyarar Firaministan Kasar Tsibiran Solomon A Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana Ga Kasar

Dangane da aukuwar lamarin, daga ranar 11 zuwa 12 ga wata, an gudanar da muhawara ta gaggawa a gun taron majalisar kula da hakkin dan Adam ta MDD karo na 53, inda zaunannen wakilin kasar Sin a ofishin MDD da ke Geneva ya yi Allah wadai da aukuwar lamarin da kakkausar murya, ya ce, a kullum kasar Sin na ganin cewa, ya kamata a yayata akidar martaba juna, da tafiya tare da dukkanin sassa, da koyi da juna tsakanin mabanbantan al’ummu, kuma tana tsayawa tsayin daka a kan kin yarda da nuna kyamar musulunci.

Lamarin da ya faru a kasar Sweden ba shi ne karo na farko ba. A cikin ’yan shekarun baya, a yayin da ake ta kara samun rikici a tsakanin sassan duniya, wasu ’yan siyasar kasashen yammacin duniya na ta kara tunzura fito na fito tsakanin al’ummu da wayewar kansu. Idan ba a manta ba, mujallar Charlie Hebdo ta Faransa ta sha wallafa zanen barkwanci da suka tada sabani a tsakanin addinai da kabilu daban daban. Tun daga watan Agustan shekarar 2020, sau da dama, wasu tsirarrun ’yan siyasar Turai sun kona Alkur’ani mai tsarki a fili. A watan Janairun shekarar 2017, gwamnatin kasar Amurka ta kaddamar da dokar kayyade shigar da al’ummar kasashen musulmi kasar, matakin da ya sa ta zama kasa daya tilo a duniya da ta sanya haramci kan rukunin al’ummar musulmi. Duk wadannan lamura sun tunzura kiyayya a tsakanin mabambantan al’ummu, tare da tsananta rashin fahimtar juna a tsakanin kabilu daban daban, kuma ainihin dalilin da ya sa haka shi ne yadda kasashen yammacin duniya ke nuna bambanci ga irin al’ummun da ba nasu ba, wadanda a ganinsu, wayewar kai na yammacin duniya ya fi na sauran sassan duniya.

Kasar Sin a nata bangaren, tana ganin cewa, duk da bambance bambance da ke tsakanin wayewar kai iri iri, amma babu wani da ya fi wani na daban, don haka ma, kullum take kira da a kiyaye kasancewar mabambantan wayewar kai, tare da sa kaimin yin musaya a tsakaninsu. Kuma hakan ya faru ne sakamakon yadda kasar Sin ta kasance kasar da ke da kabilu da dama tun fil azal, wadanda suka yi ta zaman cude-ni-in-cude-ka a tsawon tarihi na kasar, a yayin da kuma suka yi ta yin musayar wayewar kansu tare da samun ci gaba tare. Baya ga haka kuma, addinai da dama, ciki har da addinin Buddah, da Musulunci da Kirisita duk sun shigo nan kasar har sun samu bunkasa sun zama muhimman bangarori na wayewar kan kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Sabo da irin wannan akidar martaba mabambantan wayewar kai da kasar Sin ke da shi, a watan Maris na wannan shekara, kasar ta gabatar da shawarar bunkasa wayewar kai tsakanin al’ummun kasa da kasa, inda ta yi kira da a aiwatar da manufofin daidaito, da koyi da juna, da tattaunawa, da tafiya tare tsakanin dukkanin wayewar kan al’ummun duniya.

Wayewar kan musulunci ta bayar da gagarumar gudummawa ga ci gaban duniya, kuma an sha yin musaya a tsakanin wayewar kan al’ummar kasar Sin da na musulunci, matakin da ya zama misali na yin musaya a tsakanin wayewar kai daban daban. Kawo yanzu, kasar Sin da kasashen musulmi sun gudanar da taron kara wa juna sani game da wayewar kan juna har sau hudu. A ranar 15 ga watan Maris na shekarar 2022 kuma, kasar Sin ta sa kaimi ga taron MDD ya zartas da kudurin tsai da ranar 15 ga watan Maris na kowace shekara a matsayin “ranar duniya ta adawa da kyamar musulunci”.

Kasancewar bambance-bambance dake tsakanin wayewar kai daban daban, shi ya sa suke yin musaya a tsakaninsu, kuma sabo da irin musaya ne, ake samun ci gaba na bai daya, don haka muke cewa kyan wayewar kai na cikin bambance-banbancen dake akwai tsakaninsu. Muna fatan kasa da kasa za su hada hannu su yayata shawarar bunkasa wayewar kai tsakanin al’ummun kasa da kasa, don kiyaye mabambantan wayewar kan al’ummmun duniya. A sa’i daya kuma, muna fatan wasu kasashen yamma za su dauki matakai, don daidaita ainihin matsalolin nuna bambanci, kuma su karfafa fahimtar addinai da wayewar kai da ba irin nasu ba. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kulla Dangantakar Diplomasiyya Tare Da Sin, Daya Ne Daga Cikin Kudurori Mafi Dacewa Da Kasar Tsibiran Solomon Ta Tsai Da A Tarihi

Next Post

Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

12 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

13 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

14 hours ago
Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya
Daga Birnin Sin

Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya

15 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

16 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

17 hours ago
Next Post
Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.