• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

La liga Ta Zama Dandalin Masu Nuna Wariya, Cewar Vinicius

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
La liga Ta Zama Dandalin Masu Nuna Wariya, Cewar Vinicius
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid, Binicius Jnr, ya bayyana cewa gasar La liga da a baya aka santa da ‘yan wasa irinsu Ronaldinho da Ronaldo da Cristiano da Messi yanzu ta koma gasar masu nuna wariya a duniya.

Dan wasan ya bayyana haka ne bayan da magoya bayan Balencia suka dinga furta masa kalaman nuna wariya a wasan da Real madrid ta yi rashin nasara a hannun Balencia da ci 1-0 a gasar La liga da suka buga a ranar Lahadin da ta gabata.

  • Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Sai dai shima kociyan Real Madrid, Carlo Ancelotti ya ce La Liga tana da matsalar kalaman wariya, bayan da aka ci zarafin dan wasansa Binicius Junior a Balencia ranar Lahadin.

An bai wa dan kwallon na Brazil, mai shekara 22 jan kati a minti na 97, bayan cacar baki mai zafi da shi da Hugo Duro, sai dai tun farko an ja hankalin alkalin wasan, domin ya umarci magoya bayan Balencia su dakatar da kalaman wariya da suke yi wa dan kwallon Real Madrid din.

”Wannan abin da muka gani ba abin da za mu amince bane domin gabaki dayan filin wasa na rera kalaman wariya,” kamar yadda mai koyarwa Carlo Ancelotti ya sanar da jarisar Mobistar Plus.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

Ya kara da cewa ”Bana son yin magana a kan kwallon kafa domin ba wani amfani a yi magana a kan ta kuma na sanar da alkalin wasan da ya kamata ya tsayar da karawar.”
Ya ci gaba da cewa La Liga tana tare da babbar matsala domin shi a wajensa Binicius dan kwallo ne mai mahimmaci a duniya saboda haka ya kamata a dakatar da wannan halayyar a lokacin wasanni.

Binicius, wanda karon farko kenan da aka yi masa jan kati a tarihinsa na kwallon kafa, ya fuskanci kalaman wariya da na cin zarafi karo da dama a La Liga a kakar nan kuma a wannan karon an dakatar da wasa a zagaye na biyu, bayan da dan kwallon ya nuna bacin ransa kan kalaman wariyar da ake rerawa.

Daga lokacin ne ransa ya baci har ta kai da aka yi masa jan kati a fafatawar da aka ci Real 1-0, karo na takwas da ta yi rashin nasara a La Liga a bana amma Balencia, wadda ta ci wasan ta yi sama zuwa ta 13 da tazarar maki biyar tsakaninta da ‘yan ukun karshen teburin La Liga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Son Raba Gajiya Daga Bude Kofofin Ta Na Kasuwannin Gida Tare Da Kamfanonin Kasashe Daban-Daban

Next Post

“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

17 hours ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

23 hours ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

2 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

3 days ago
Shekaru 15, Wasanni 578, Daga Karshe Harry Kane Ya Lashe Kofi
Wasanni

Shekaru 15, Wasanni 578, Daga Karshe Harry Kane Ya Lashe Kofi

4 days ago
Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot
Wasanni

Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot

5 days ago
Next Post
“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari

“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.