• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

La liga Ta Zama Dandalin Masu Nuna Wariya, Cewar Vinicius

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Vinicius

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid, Binicius Jnr, ya bayyana cewa gasar La liga da a baya aka santa da ‘yan wasa irinsu Ronaldinho da Ronaldo da Cristiano da Messi yanzu ta koma gasar masu nuna wariya a duniya.

Dan wasan ya bayyana haka ne bayan da magoya bayan Balencia suka dinga furta masa kalaman nuna wariya a wasan da Real madrid ta yi rashin nasara a hannun Balencia da ci 1-0 a gasar La liga da suka buga a ranar Lahadin da ta gabata.

  • Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Sai dai shima kociyan Real Madrid, Carlo Ancelotti ya ce La Liga tana da matsalar kalaman wariya, bayan da aka ci zarafin dan wasansa Binicius Junior a Balencia ranar Lahadin.

An bai wa dan kwallon na Brazil, mai shekara 22 jan kati a minti na 97, bayan cacar baki mai zafi da shi da Hugo Duro, sai dai tun farko an ja hankalin alkalin wasan, domin ya umarci magoya bayan Balencia su dakatar da kalaman wariya da suke yi wa dan kwallon Real Madrid din.

”Wannan abin da muka gani ba abin da za mu amince bane domin gabaki dayan filin wasa na rera kalaman wariya,” kamar yadda mai koyarwa Carlo Ancelotti ya sanar da jarisar Mobistar Plus.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

Ya kara da cewa ”Bana son yin magana a kan kwallon kafa domin ba wani amfani a yi magana a kan ta kuma na sanar da alkalin wasan da ya kamata ya tsayar da karawar.”
Ya ci gaba da cewa La Liga tana tare da babbar matsala domin shi a wajensa Binicius dan kwallo ne mai mahimmaci a duniya saboda haka ya kamata a dakatar da wannan halayyar a lokacin wasanni.

Binicius, wanda karon farko kenan da aka yi masa jan kati a tarihinsa na kwallon kafa, ya fuskanci kalaman wariya da na cin zarafi karo da dama a La Liga a kakar nan kuma a wannan karon an dakatar da wasa a zagaye na biyu, bayan da dan kwallon ya nuna bacin ransa kan kalaman wariyar da ake rerawa.

Daga lokacin ne ransa ya baci har ta kai da aka yi masa jan kati a fafatawar da aka ci Real 1-0, karo na takwas da ta yi rashin nasara a La Liga a bana amma Balencia, wadda ta ci wasan ta yi sama zuwa ta 13 da tazarar maki biyar tsakaninta da ‘yan ukun karshen teburin La Liga.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu
Manyan Labarai

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle
Wasanni

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

October 25, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana
Wasanni

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Next Post
“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari

“Magance Hadari”? “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki Da Sin Shi Ne Hadari

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.