• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labarin Ƙarya: Babu Inda Gwamna Dauda Lawal Ya Kashe Naira Miliyan 400 Don Tafiye-tafiye

by Sulaiman
2 years ago
Dauda

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya ƙaryata zargin da a ke masa na cewa ya kashe sama da Naira Miliyan 400 a fannin tafiye-tafiyensa zuwa ƙasashen waje. 

Mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu ya bayyana wannan labari, wanda ya samo asali daga wata jaridar yanar gizo, a matsayin wani shirri da aka tsara da gangan don a ɗauke hankalin gwamnatin.

  • Gwamnatin Kano Ta Mayar Da Daliban Borno Gida Bayan Kammala Karatunsu A Kano
  • Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

Kakakin Gwamnan ya bayyana cewa, “Wata jaridar yanar gizo ce ta kawo labarin wai Gwamna Lawal ya kashe N170,276,294.31 a fita ƙasar nan, sannan ya kashe N221,567,094 a tafiye-tafiyen cikin ƙasa, sannan ya kashe N6,929,500.00 a tsaro na musaman a cikin watanni uku.

Ya ce, wannan kuskuren fahimtar ya samo asali ne bisa murguɗe jadawalin kasafin kuɗi, alhali sun manta kashi na farko na shekara, na biyu da na uku, duk sun faɗo ne a gwamnatin da ta gabata.

Sanarwar ta Sulaiman, ta ce, “Mun ga wani rahoto da ya yi zargin cewa Gwamna Dauda Lawal ya kashe sama da Naira Miliya. 400 kan tafiye-tafiyen ƙasashen waje. Wannan ƙarya ce da nufin ci wa Gwamnan mutunci.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

Ya ci gaba da cewa, yin komai a bayyane, ita ce silar gwamnatin Dauda Lawal. Duk wani bayani da a ke nema, za a iya samu a manhajar gwamnatin ta yanar gizo a zamfara.gov.ng.

Yana mai cewa, su a wannan manhaja ta gwamnatin jihar, akwai cikakkun bayanai game da yadda gwamnatin ke tafiyar da kasafin ta, wanda kuma ke ƙunshe da abubuwan da Gwamnan ke kashewa a tafiye-tafiye dalla-dalla.

Ya ce, “A gwamnatin Dauda Lawal, muna da cikakken tsarin yin komai a bayyane, ta yadda babu wata kafa da za a yi almundahana da kuɗaɗen gwamnati.”

Da ya ke bayani game da tafiye-tafiyen da Gwamnan ya yi kuwa, Idris cewa ya yi tafiye-tafiyen aiki uku ne kawai Dauda Lawal ya yi tun da ya karɓi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya ce, “Tafiye-tafiyen ayyuka uku da ya yi, su ne: Halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya a ƙasar Amurka; Wani taron ƙara wa juna sani na ƙungiyar ‘United Nations Development Programme (UNDP) a garin Kigali na ƙasa Ruwanda; da kuma taron da ya yi da Shugaban Bankin ci gaban Afrika, Dr Akinwumi A. Adesina a Abidjan ta ƙasar Kodebuwa.”

Ya ci gaba da bayyana cewa, “Bugu da ƙari, taron da ya halarta a Kigali, ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya ne ta shirya shi, sannan ƙungiyar ‘United Nations Development Programme (UNDP)’ ta ɗauki nauyin taron. Don haka babu ko kwabon da gwamnati ta kashe a kai. Inda aka kashe kuɗi a tafiye-tafiyen, biyu ne kawai na Majalisar Ɗinkin Duniya na Amerika da wanda Gwamnonin yankin Arewa maso Yamma suka gudanar da Shugaban bankin AfDB a Abidjan.”

Sanarwar ta ce, masu wancan labari, sun yi kuskuren ɗora kuɗaɗen da waccan gwamnatin ta kashe ne a kan gwamnatin mu. Babu inda Gwamnatin mu ta ɗauki wasu jami’an tsaron na kanta, ba su kuma yi wani watan Ramadan a kan mulki ba. Don haka mun kasa gane yadda aka jingina mana kuɗaɗen da aka kashe a watan Ramadana da na salla ƙarama.”

Ya ce, su a gwamnatin su, sun samu jajircewa wajen gudanar harkokin gwamnati a bayyane, a fili babu muna-muna. “Mun yi wa Zamfarawa alƙawarin kawo canji mai ma’ana, kuma a kan haka muka tsayu don cika allawari. Tsarin gwamnatin mu na ceto al’umma, cikakken tsari ne da ya shafi kowane fanni na gwamnati, babu wani murguɗaɗɗen labarin da zai kawo mana cikas,” in ji Kakakin Gwamnan.

 

 

 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
Labarai

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Bude Taron Karawa Juna Sani Game Da Kasar Sin

Shugaba Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Bude Taron Karawa Juna Sani Game Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.