• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labarin Ƙarya: Babu Inda Gwamna Dauda Lawal Ya Kashe Naira Miliyan 400 Don Tafiye-tafiye

by Sulaiman
2 years ago
Dauda

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya ƙaryata zargin da a ke masa na cewa ya kashe sama da Naira Miliyan 400 a fannin tafiye-tafiyensa zuwa ƙasashen waje. 

Mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu ya bayyana wannan labari, wanda ya samo asali daga wata jaridar yanar gizo, a matsayin wani shirri da aka tsara da gangan don a ɗauke hankalin gwamnatin.

  • Gwamnatin Kano Ta Mayar Da Daliban Borno Gida Bayan Kammala Karatunsu A Kano
  • Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

Kakakin Gwamnan ya bayyana cewa, “Wata jaridar yanar gizo ce ta kawo labarin wai Gwamna Lawal ya kashe N170,276,294.31 a fita ƙasar nan, sannan ya kashe N221,567,094 a tafiye-tafiyen cikin ƙasa, sannan ya kashe N6,929,500.00 a tsaro na musaman a cikin watanni uku.

Ya ce, wannan kuskuren fahimtar ya samo asali ne bisa murguɗe jadawalin kasafin kuɗi, alhali sun manta kashi na farko na shekara, na biyu da na uku, duk sun faɗo ne a gwamnatin da ta gabata.

Sanarwar ta Sulaiman, ta ce, “Mun ga wani rahoto da ya yi zargin cewa Gwamna Dauda Lawal ya kashe sama da Naira Miliya. 400 kan tafiye-tafiyen ƙasashen waje. Wannan ƙarya ce da nufin ci wa Gwamnan mutunci.”

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Ya ci gaba da cewa, yin komai a bayyane, ita ce silar gwamnatin Dauda Lawal. Duk wani bayani da a ke nema, za a iya samu a manhajar gwamnatin ta yanar gizo a zamfara.gov.ng.

Yana mai cewa, su a wannan manhaja ta gwamnatin jihar, akwai cikakkun bayanai game da yadda gwamnatin ke tafiyar da kasafin ta, wanda kuma ke ƙunshe da abubuwan da Gwamnan ke kashewa a tafiye-tafiye dalla-dalla.

Ya ce, “A gwamnatin Dauda Lawal, muna da cikakken tsarin yin komai a bayyane, ta yadda babu wata kafa da za a yi almundahana da kuɗaɗen gwamnati.”

Da ya ke bayani game da tafiye-tafiyen da Gwamnan ya yi kuwa, Idris cewa ya yi tafiye-tafiyen aiki uku ne kawai Dauda Lawal ya yi tun da ya karɓi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya ce, “Tafiye-tafiyen ayyuka uku da ya yi, su ne: Halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya a ƙasar Amurka; Wani taron ƙara wa juna sani na ƙungiyar ‘United Nations Development Programme (UNDP) a garin Kigali na ƙasa Ruwanda; da kuma taron da ya yi da Shugaban Bankin ci gaban Afrika, Dr Akinwumi A. Adesina a Abidjan ta ƙasar Kodebuwa.”

Ya ci gaba da bayyana cewa, “Bugu da ƙari, taron da ya halarta a Kigali, ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya ne ta shirya shi, sannan ƙungiyar ‘United Nations Development Programme (UNDP)’ ta ɗauki nauyin taron. Don haka babu ko kwabon da gwamnati ta kashe a kai. Inda aka kashe kuɗi a tafiye-tafiyen, biyu ne kawai na Majalisar Ɗinkin Duniya na Amerika da wanda Gwamnonin yankin Arewa maso Yamma suka gudanar da Shugaban bankin AfDB a Abidjan.”

Sanarwar ta ce, masu wancan labari, sun yi kuskuren ɗora kuɗaɗen da waccan gwamnatin ta kashe ne a kan gwamnatin mu. Babu inda Gwamnatin mu ta ɗauki wasu jami’an tsaron na kanta, ba su kuma yi wani watan Ramadan a kan mulki ba. Don haka mun kasa gane yadda aka jingina mana kuɗaɗen da aka kashe a watan Ramadana da na salla ƙarama.”

Ya ce, su a gwamnatin su, sun samu jajircewa wajen gudanar harkokin gwamnati a bayyane, a fili babu muna-muna. “Mun yi wa Zamfarawa alƙawarin kawo canji mai ma’ana, kuma a kan haka muka tsayu don cika allawari. Tsarin gwamnatin mu na ceto al’umma, cikakken tsari ne da ya shafi kowane fanni na gwamnati, babu wani murguɗaɗɗen labarin da zai kawo mana cikas,” in ji Kakakin Gwamnan.

 

 

 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Bude Taron Karawa Juna Sani Game Da Kasar Sin

Shugaba Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Bude Taron Karawa Juna Sani Game Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.