ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labarin Ƙarya: Babu Inda Gwamna Dauda Lawal Ya Kashe Naira Miliyan 400 Don Tafiye-tafiye

by Sulaiman
3 years ago
Dauda

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya ƙaryata zargin da a ke masa na cewa ya kashe sama da Naira Miliyan 400 a fannin tafiye-tafiyensa zuwa ƙasashen waje. 

Mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu ya bayyana wannan labari, wanda ya samo asali daga wata jaridar yanar gizo, a matsayin wani shirri da aka tsara da gangan don a ɗauke hankalin gwamnatin.

  • Gwamnatin Kano Ta Mayar Da Daliban Borno Gida Bayan Kammala Karatunsu A Kano
  • Za A Fuskanci Karancin Motoci A Nijeriya Sakamakon Karin Haraji

Kakakin Gwamnan ya bayyana cewa, “Wata jaridar yanar gizo ce ta kawo labarin wai Gwamna Lawal ya kashe N170,276,294.31 a fita ƙasar nan, sannan ya kashe N221,567,094 a tafiye-tafiyen cikin ƙasa, sannan ya kashe N6,929,500.00 a tsaro na musaman a cikin watanni uku.

ADVERTISEMENT

Ya ce, wannan kuskuren fahimtar ya samo asali ne bisa murguɗe jadawalin kasafin kuɗi, alhali sun manta kashi na farko na shekara, na biyu da na uku, duk sun faɗo ne a gwamnatin da ta gabata.

Sanarwar ta Sulaiman, ta ce, “Mun ga wani rahoto da ya yi zargin cewa Gwamna Dauda Lawal ya kashe sama da Naira Miliya. 400 kan tafiye-tafiyen ƙasashen waje. Wannan ƙarya ce da nufin ci wa Gwamnan mutunci.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ya ci gaba da cewa, yin komai a bayyane, ita ce silar gwamnatin Dauda Lawal. Duk wani bayani da a ke nema, za a iya samu a manhajar gwamnatin ta yanar gizo a zamfara.gov.ng.

Yana mai cewa, su a wannan manhaja ta gwamnatin jihar, akwai cikakkun bayanai game da yadda gwamnatin ke tafiyar da kasafin ta, wanda kuma ke ƙunshe da abubuwan da Gwamnan ke kashewa a tafiye-tafiye dalla-dalla.

Ya ce, “A gwamnatin Dauda Lawal, muna da cikakken tsarin yin komai a bayyane, ta yadda babu wata kafa da za a yi almundahana da kuɗaɗen gwamnati.”

Da ya ke bayani game da tafiye-tafiyen da Gwamnan ya yi kuwa, Idris cewa ya yi tafiye-tafiyen aiki uku ne kawai Dauda Lawal ya yi tun da ya karɓi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya ce, “Tafiye-tafiyen ayyuka uku da ya yi, su ne: Halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya a ƙasar Amurka; Wani taron ƙara wa juna sani na ƙungiyar ‘United Nations Development Programme (UNDP) a garin Kigali na ƙasa Ruwanda; da kuma taron da ya yi da Shugaban Bankin ci gaban Afrika, Dr Akinwumi A. Adesina a Abidjan ta ƙasar Kodebuwa.”

Ya ci gaba da bayyana cewa, “Bugu da ƙari, taron da ya halarta a Kigali, ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya ne ta shirya shi, sannan ƙungiyar ‘United Nations Development Programme (UNDP)’ ta ɗauki nauyin taron. Don haka babu ko kwabon da gwamnati ta kashe a kai. Inda aka kashe kuɗi a tafiye-tafiyen, biyu ne kawai na Majalisar Ɗinkin Duniya na Amerika da wanda Gwamnonin yankin Arewa maso Yamma suka gudanar da Shugaban bankin AfDB a Abidjan.”

Sanarwar ta ce, masu wancan labari, sun yi kuskuren ɗora kuɗaɗen da waccan gwamnatin ta kashe ne a kan gwamnatin mu. Babu inda Gwamnatin mu ta ɗauki wasu jami’an tsaron na kanta, ba su kuma yi wani watan Ramadan a kan mulki ba. Don haka mun kasa gane yadda aka jingina mana kuɗaɗen da aka kashe a watan Ramadana da na salla ƙarama.”

Ya ce, su a gwamnatin su, sun samu jajircewa wajen gudanar harkokin gwamnati a bayyane, a fili babu muna-muna. “Mun yi wa Zamfarawa alƙawarin kawo canji mai ma’ana, kuma a kan haka muka tsayu don cika allawari. Tsarin gwamnatin mu na ceto al’umma, cikakken tsari ne da ya shafi kowane fanni na gwamnati, babu wani murguɗaɗɗen labarin da zai kawo mana cikas,” in ji Kakakin Gwamnan.

 

 

 

 

 

Dauda
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Bude Taron Karawa Juna Sani Game Da Kasar Sin

Shugaba Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Bude Taron Karawa Juna Sani Game Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.