• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
Jonathan

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya bayyana cewa lalacewar tsarin zabe babbar barazana ce ga dorewar dimokuradiyya a Nahiyar Afirka.

Tsohon shugaban kasa ya ce sai masu ruwa da tsaki sun hada kai wajen sauya tsarin zabe, in ba haka ba tsarin dimokuradiyya na iya rushewa a wannan yanki.

  • Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

Jonathan ya bayyana hakan ne a lokacin taron tattaunawa kan dimokuradiyya da gidauniyar Goodluck Jonathan ta shirya a Accra, babban birnin kasar Ghana, tsohon shugaban kasa ya bukaci shugabannin siyasa su yi kokarin sanya dimokuradiyya ta tabbatar da kyakkyawan makoma ga matasa masu tasowa, wanda muryoyinsu ke da muhimmanci.

Rahotannin dai sun bayyana cewa jam’iyyar PDP na tunanin bai wa Jonathan tikitin takarar shuugaban kasa a zaben 2027.

Jonathan ya karbi shugabancin Nijeriya a shekarar 2010, bayan rasuwar tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’adua. Ya yi takara a zaben shugaban kasa na 2011 karkashin jam’iyyar PDP kuma ya samu nasara.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Haka kuma, ya fadi zaben shugaban kasa na 2015 ga dan takarar jam’iyyar APC, Marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a watan Yuli na wannan shekara.

Akwai zazzafar muhawara kan dokar da ta bai wa Jonathan damar sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027, tsohon gwamnan Jihar Jigawa kuma daya daga cikin shahararrun jiga-jigan jam’iyyar PDP, Sule Lamido, a kwanan nan ya bayyana Jonathan a matsayin mafi kyawun dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2027.

Lamido ya kuma yi kira da shugabancin jam’iyyar na kasa su yi kokarin tabbatar da an tsayar da shi takarar shugaban kasa a 2027.

Jonathan ya ce, “Dimokuradiyya a Nahiyar Afirka na fuskantar babbar barazana, sannan ta kusa da rushewa sai dai masu ruwa da tsaki sun hada kai kafin su iya ceton ta daga wannan babbar barazana. Lalata tsarin zabe na ci gaba da kasancewa daya daga cikin manyan barazanar da ke cikin Afirka.

“Mu a Afirka dole ne mu fara duba dimokuradiyyarmu da kuma sake tunani kan hanyar da za ta yi mana aiki da kyau da mutanenmu. Daya daga cikin manyan matsalolin shi ne, tsarin zabenmu. Mutane suna amfani da hanyoyin damfara don ci gaba da kasancewa a mulki ta kowanne hanya.

“Idan muna iya gudanar da sahihin zabe, duk shugaba da ya gaza yin aiki za a kayar da shi daga kan mulki. Amma a cikin al’amuranmu, mutane suna amfani da tsarin zabe domin su ci gaba da zama a kan kujerar mulki duk da cewa mutane ba sa son su.

“Mutanenmu na son samun ‘yancinsu. Suna son kuri’unsu su yi tasiri a lokacin zabe. Suna son wakilci bisa adalci da samun hadin kai.

“Suna son ingantaccen ilimi. Mutanenmu suna son tsaro da samun ingantaccen kiwon lafiya. Suna son a ba su aikin yi. Suna son a ba su daraja. Lokacin da shugabanni suka kasa cika wadannan bukatun, mutane ba sa son haka,” in ji Jonathan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.