• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lallai A Rika Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Lallai A Rika Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Kamar yadda ya faru a manyan zabukan da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabarairu da ranar 18 ga watan Maris 2023, a zaben kujerar gwamna da aka yi kwanan nan a Jihohin Kogi da Imo da Bayelsa ma an tafka rikice-rikice har ya kai ga rasa rayuka. An kuma samu rahotannin saye da sayarwar kuri’u, sace-sacen akwatin zabe da kuma wasu rahotannin na arcewa da na’urar zabe ta BBAS.

Kamar yadda aka zata, korafe-korafen da ke tafiya kotun sauraron kararrakin zabe sai karuwa suke yi amma kuma wadanda suka aikata laifukan zaben suna yawo a tituna abin su, ba tare da an gurfanar da su a gaban kuliya ba. Sakamakon zabukan da aka yi ya gamu da shakku sannan INEC na fuskantar rasa kima da mutuncinta a idanun ‘yan kasa, a daidai lokacin da ake kara kira na a tabbatar da hukunci a kan masu aikata laifukan zabe.

  • Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Dabarun Warware Rikicin Isra’ila Da Falasdinawa
  • Al’ummun Amurka Sun Yi Kira Ga Kyautata Dangantaka Tsakanin Sin Da Amurka

Duk da ya kamata a lura cewa, an gabatar da wasu sauye-sauye a dokokin zabe bisa yadda aka bukata bayan zaben shekarar 2019 kamar yadda ake iya gani a dokar zabe ta shekarar 2022, amma sarkakiyar da ake ganin ta sarke zabuka da sakamakonsu a Nijeriya su ne yadda masu aikata laifukan zabe ke cin karensu ba babbaka da kuma rashin hukunta su.

Bayan kammala zaben shugaban kasa da na majalisun kasa na ranar 25 ga Fabarairu, nan take shugaban rundunar ‘yansanda na lokacin, Usman Baba, a taron da ya yi da manyan hafsoshin rundunar a Abuja, ya bayyana cewa, rundunar ta samu nasarar kai dauki a korafe-korafen zabe 185, sun kuma kama masu aikata laifukan zabe har mutum 203 tare da kama makamai 18.

“Haka kuma an kama masu laifukan zabe 304 a yayin zabukan gwamna da na ‘yan majalisun jihohi da aka cafke masu aikata laifuka 578 da makamai 48.

“Wannan ya hada da masu laifi 161 a Jihar Kano, 45 a Jihar Legas, 49  a Jihar Sakkwato, 16 a Jihar Kuros Ribas, 22 a Jihar Jigawa, 17 a Jihar Nasarawa da kuma mutum 18 a Jihar Oyo, da sauransu”.

Ya kuma bayyana cewa, rudunar ta ci gaba da bincike a kan laifukan a sashin kula laifukan zabe, inda aka ce za a aika su sashin shari’a na hukumar zabe daga nan ne za su gabatar da su a gaban kotu don hukutansu.

Tsohon shugaban rundunar ‘yansanda ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa, za su hada kai da hukumar zabe don tabbatar da an hukunta dukkan wadanda aka samu da aikata laifukan zabe ba tare da bata lokaci ba don tabbatar da adalci kuma haka ya zama darasi da tsaftace tsarin dimokuradiyyar Nijeriya.”

A zabukan da aka gudanar kwanan nan, kungiyoyi masu zaman kansu da suka sa ido, da dama sun bayar da rahoton yadda masu rike da madafun iko suka yi amfani da mukamansu wajen murde zabe da yadda ‘yansiyasa suka yi ta saye da sayar da kuri’u da kuma yadda wasu hukumomi kamar INEC, jam’iyyun siyasa da rundunonin tsaro suka kasa yin aikin su yadda ya kamata a daidai lokacin da ake tafka wadannan laifukan.

A dakin tattara bayanan yadda ake gudanar da zabukan na kungiyoyi masu zaman kansu, sun bayar da rahotannin yadda aka yi cuwa-cuwar zabe da yadda aka jirkita sakamakon zabukkan gwamna da aka yi a jihoji uku wanda a cewarsu hakan na iya jefa ayar tambaya a kan inganci da sahihancin zaben gaba daya da ma makomar tsarin dimokuradiyya a Nijeriya.

‘Yan Nijeriya sun zaci masu ruwa da staki za su dauki darasi daga zabukkan da aka yi a baya, musamman an sa rai INEC za ta kara inganta ayyukanta a zabukan da aka yi kwanan nan amma hakan bai yiwu ba don zabukan ma sun zama abin takaici.

Zabukan gwamna da aka yi a wadannan jihohin tamkar wani babban koma baya ne ga tsarin dimokurudiyya a Nijeriya.

Tun da aka fara jumhuriyya ta biyu a shekarar 1999, duk wani zabe da aka yi ya fuskanci matsaloli na laifukan zabe da dama.

Zabukan da suka biyo baya a tarayya, jihohi da kananan hukumomi sun fuskanci matsaloli da dama inda ‘yansiyasa ke rungumar tashin hankali don biyan bukatunsu.

Tabbas laifukan zabe sun kasance babbar barazana ga gabatar da sahihin zabe a Nijeriya musamman ganin suna kaiwa ga tayar hankali da kasshe-kashe a wasu lokuta.

Yayin da wasu masu lura da al’amuran yau da kullum suke da ra’ayin cewa tsarin shari’armu ne ke da rauni, wasu kuma na ganin ba zai yiwu a ce INEC, a matsayinta ta mai gudanar da zabe ta zama wadda za ta gurfanar tare da hukunta masu laifukan zabe ba.

A wata mukala da ya gabatar a zauren ‘Chatham House’ da ke Landan, shugaban INEC, Farfesa Yakubu Mahmoud ya bayyana yadda hukumar ta gaza wajen hukunta masu laifukan zabe.

Ya ce: “Duk da doka dokar zabe ta ba hukuma ikon hukunta masu laifukan zabe, amma hukumar ba ta da karfi da kayan aikin kamawa tare da gudanar da bincike yadda kamata don tabbatar da hukunta masu aikata laifukan zabe.”

“A kan haka INEC take goyon bayan kafa Hukumar Hukunta masu laifukan Zabe da kotun musamman ta hukunta masu laifukan zabe, kamar yadda wasu kwamitocin da gwamnatin tarayya ta kafa suka bayar da shawara, musamman kwamitin Uwais na shekarar 2009, da kwamitin Lemu na shekarar 2011 da kuma kwanitin Nnamani na shakarar 2017.”

A bara, wannan jaridar ta nemi majalisar kasa ta gagguta zartar da dokar laifukan zabe ta shekarar 2021 don tsohon shugaban kasa Buhari ya sanya hannu.

Da an sanya wa dokar hannu da ta karfafi hukumar zabe wajen gudanar da binciken masu laifukan zabe tare da hukunta su, dokar ta kuma yi tanadin daurin shekara 20 ga duk wanda aka samu da laifin sace akwatin zabe a yayin da ake gudanar da zabe.

A ra’ayinmu, ba zai yiwu Nijeriya ta ci gaba da jiran majalisar kasa a kan zartar da dokar laifukan zaben ba musamman ganin kamar majalisar ba ta da sha’awa a kan dokar, kuma ga shi wadanda suka aikata laifukan zaben na yawatawa ba tare da an hukunta su ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’ummun Amurka Sun Yi Kira Ga Kyautata Dangantaka Tsakanin Sin Da Amurka

Next Post

Shari’ar Zaben Gwamnoni: Kallo Ya Koma Kotun Koli

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

18 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
Shari’ar Zaben Gwamnoni: Kallo Ya Koma Kotun Koli

Shari'ar Zaben Gwamnoni: Kallo Ya Koma Kotun Koli

LABARAI MASU NASABA

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.