• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lampard Ya Zama Sabon Kocin Chelsea

by Sadiq
3 years ago
Chelsea

Frank Lampard ya zama kocin Chelsea na rikon kwarya zuwa karshen kakar wasanni ta bana, bayan shekara biyu da korarsa.

Tsohon dan wasan Chelsea ya horar da kungiyar tsakanin Yulin 2019 zuwa Janairun 2021, wanda Thomas Tuchel ya maye gurbinsa.

  • Hukumar NAFDAC Ta Bankado Magunguna Marasa Rajista Na Naira Miliyan 15 A Abuja
  • Wata Kungiyar Mata Musulmi Ta Nuna Takaicinta Kan Yawaitar Mutuwar Aure A Arewa

Ranar Lahadi Chelsea ta sallami Graham Potter, wanda ya maye gurbin Tuchel a Stamford Bridge.

Chelsea tana mataki na 11 a teburin gasar Firimiya, bayan yin kunnen doki da Liverpool a ranar Talata.

Bruno Saltor ne ya ja ragamar Chelsea a karawar – Lampard, mai shekara 44 ya kalli wasan na hamayya a ranar a Stamford Bridge.

LABARAI MASU NASABA

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

Chelsea wadda ta kashe sama da £550m wajen sayo sabbin ‘yan wasa tana da tazarar maki 11 tsakaninta da ta hudu a gasar.

Kenan da kyar za ta buga Gasar zakarun Turai a badi, idan ba ta lashe na bana ba, bayan da ta kasa shiga ‘yan hudun farko kawo yanzu.

A zaman farko da Lampard ya horar a Chelsea ya lashe FA Cup da ya gudanar da aikin.

Lampard – wanda shine kan gaba a ci wa kungiyar kwallaye a lokacin da ya buga wa Chelsea tamaula – ya ci wasa 44 daga 84 a matakin koci.

Daga baya aka doke shi wasa biyar daga takwas a lik, fiye da fafatawa 23 a baya, hakan ya sa ya rasa aikinsa na mai horar da kungiyar Stamford Bridge.

Lampard bai da wata kungiya da yake jan ragama a yanzu haka, tun bayan da Everton ta sallame shi a Janairu, kasa da shekara daya a Goodison Park.

Ranar Asabar Chelsea za ta je Wolverhampton a gasar Firimiya, sannan ta ziyarci Real Madrid a wasan farko a quarter finals a Sifaniya ranar 12 ga watan Afirilu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
Wasanni

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

October 12, 2025
Kofin Duniya
Wasanni

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

October 12, 2025
Next Post
An Cafke Wata Mata Bisa Zargin Sace Kwandunan Tumatir A Kwara

An Cafke Wata Mata Bisa Zargin Sace Kwandunan Tumatir A Kwara

LABARAI MASU NASABA

hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025
Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.