• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lawan Ya Zama Shugaban Majalisar Dokokin Borno Karo Na 4 A Jere

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Lawan Ya Zama Shugaban Majalisar Dokokin Borno Karo Na 4 A Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar dokokin jihar Borno ta zabi Abdulkarim Lawan a matsayin shugaban majalisar ta 10.

Honarabul Lawan dai shi ne tsohon kakakin majalisa ta tara kuma ya kasance yana jagorantar majalisar tun a majalisa ta shida.

  • Sanata Barau Ya Zama Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa
  • Falgore Ya Zama Shugaban Majalisar Dokokin Kano

Magatakardar majalisar, Jidayi Mamza ya sanar da cewa majalisar ta samu sanarwa daga gwamnan jihar Babagana Zulum, na gudanar da zamanta na farko a ranar 13 ga watan Yuni.

“Majalissar ta samu sako daga mai girma gwamnan jihar Borno Babagana Zulum, yana bukatar ta gudanar da zamanta na farko a ranar Talata 13 ga watan Yuni 2023 bisa la’akari da ikon da aka ba shi a sashe na 105 karamin sashe na 3 na kundin tsarin mulkin 1999,” in ji shi.

Zababben dan majalisar mai wakiltar Marte, Gambomi Marte ya nemi takarar Abdulkarim Lawan sannan zababben dan majalisa mai wakiltar Jere, Abba Kyari Kolo ya mara masa baya.

Labarai Masu Nasaba

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Majalisar ta kuma zabi tsohon mataimakin kakakin majalisar Abdullahi Musa daga mazabar Askira Uba a matsayin mataimakin kakakin majalisar.

Dukkan mambobin biyu sun amince da nadin kuma sun bayyana shirin yin aiki.

A jawabinsa na karramawa jim kadan bayan rantsar da shi, Abdulkarim Lawan wanda ya shafe shekaru 12 yana shugabancin majalisar, ya yaba wa ‘yan majalisar bisa sake zabensa.

Ya kuma bukaci sabbin ‘yan kwamitin da aka kaddamar da su kara matsa kaimi tare da hada hannu da bangaren zartaswa domin kawo sauyi a jihar ta fuskar ilimi, samar da abinci, tsaro da dai sauransu.

Shugaban majalisar ya yi alkawarin aiwatar da manufar bude kofa don ciyar da majalisar zuwa wani mataki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Majalisar Dokokin BornoZabeZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bilyaminu Ismail Ya Zama Shugaban Majalisar Dokokin Zamfara Karo Na 7

Next Post

An Rantsar Da Bathiya Wesley A Matsayin Kakakin Majalisar Dokokin Adamawa

Related

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

18 minutes ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
Labarai

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

47 minutes ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2 hours ago
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

6 hours ago
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

8 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

9 hours ago
Next Post
An Rantsar Da Bathiya Wesley A Matsayin Kakakin Majalisar Dokokin Adamawa

An Rantsar Da Bathiya Wesley A Matsayin Kakakin Majalisar Dokokin Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

May 11, 2025
Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

May 11, 2025
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

May 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.