• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Layin Dogo Na Habasha Zuwa Djibouti Na Kara Habaka Hada Hadar Sufuri A Yankin Kahon Afirka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Layin Dogo Na Habasha Zuwa Djibouti Na Kara Habaka Hada Hadar Sufuri A Yankin Kahon Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Layin dogo tsakanin Habasha da Djibouti da kasar Sin ta gina, ya fara jigilar motocin daukar kaya a jiya Laraba, daga tashoshin ruwan Djibouti, zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha.

Kashin farko na motocin 63 sun isa tashar Indode dake wajen birnin Addis Ababa a jiya Laraba, kuma ministan kula da sufuri da jigila na Habasha Denge Boru, ya bayyana lamarin a matsayin muhimmin ci gaba ga yunkurin Habasha na inganta bangaren sufuri da jigila.

  • Xi Ya Bukaci A Hada Hannu Wajen Gina BRI Domin Samar Da Sabbin Damarmaki Ga Hadin Gwiwar Asiya Da Turai

A hakika, tun bayan kaddamar da layin dogo na sufurin hajoji da jama’a, wanda ya hada kasar Habasha maras iyaka da teku da kasar Djibouti a ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2018, yau sama da shekaru biyar, layin dogon na ta kara samun tagomashi, ta fannin bunkasa hada hadar sufuri, da kasuwanci tsakanin kasashen biyu, da ma kasashen dake shiyyar ta kahon Afirka.

Karkashin wannan katafaren aiki na ginin layin dogo da kasar Sin ya kammala tun a shekarar 2017, yanzu haka kasar Habasha ta samu babbar damar shigarwa, da fitar da manyan hajoji ta tashoshin jiragen ruwan na Djibouti. Har ma wasu alkaluma sun shaida yadda kaso sama da 95 bisa dari, na hajojin cinikayyar kasar Habasha ke bi ta tashoshin ruwan Djibouti.

Ko shakka babu wannan babban ci gaba ne a tarihin yankin kahon Afirka.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Muna iya gani daga sakamakon ci gaban da layin dogon ya haifar, cewa baya ga saukaka safarar hajoji, jiragen kasa dake bin layin dogon, sun kuma saukaka sufurin fasinjoji, ta hanyar rage farashin zirga zirga tsakanin sassan kasashen biyu.

Irin wadannan nasarori da layin dogon ke samu, sun tabbatar da burin da kasar Sin tare da abokan huldar ta na nahiyar Afirka ke fatan cimmawa, ta fuskar gudanar da hadin gwiwa mai dorewa, wanda ke ingiza ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummun kasashe masu tasowa.

Ko shakka ba bu layin dogo na Habasha zuwa Djibouti, na ci gaba da bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, da ma sauran kasashen yankin kahon Afirka, ta fuskar saukaka farashi, da lokacin safarar hajoji, baya ga kara inganta yanayin sufuri, da samar da karin guraben ayyukan yi ga al’ummun kasashen yankin, matakin da masharhanta ke ganin zai ci gaba da fadada cinikayya, da hada hadar shige da fice tsakanin kasashen yankin gabashin Afirka baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Bauchi Ya Rushe Majalisar Zartaswa Ta Jihar

Next Post

Awanni 24 Kafin Rantsarwa, Shugaban Rikon Kwarya A Jihar Yobe Ya Rasu

Related

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

59 minutes ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

2 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

3 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

20 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

21 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

22 hours ago
Next Post
Awanni 24 Kafin Rantsarwa, Shugaban Rikon Kwarya A Jihar Yobe Ya Rasu

Awanni 24 Kafin Rantsarwa, Shugaban Rikon Kwarya A Jihar Yobe Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon SharaÉ—i Na BuÉ—e Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon SharaÉ—i Na BuÉ—e Asusun Banki

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.