ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Layin Dogo Na Habasha Zuwa Djibouti Na Kara Habaka Hada Hadar Sufuri A Yankin Kahon Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
Habasha

Layin dogo tsakanin Habasha da Djibouti da kasar Sin ta gina, ya fara jigilar motocin daukar kaya a jiya Laraba, daga tashoshin ruwan Djibouti, zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha.

Kashin farko na motocin 63 sun isa tashar Indode dake wajen birnin Addis Ababa a jiya Laraba, kuma ministan kula da sufuri da jigila na Habasha Denge Boru, ya bayyana lamarin a matsayin muhimmin ci gaba ga yunkurin Habasha na inganta bangaren sufuri da jigila.

  • Xi Ya Bukaci A Hada Hannu Wajen Gina BRI Domin Samar Da Sabbin Damarmaki Ga Hadin Gwiwar Asiya Da Turai

A hakika, tun bayan kaddamar da layin dogo na sufurin hajoji da jama’a, wanda ya hada kasar Habasha maras iyaka da teku da kasar Djibouti a ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2018, yau sama da shekaru biyar, layin dogon na ta kara samun tagomashi, ta fannin bunkasa hada hadar sufuri, da kasuwanci tsakanin kasashen biyu, da ma kasashen dake shiyyar ta kahon Afirka.

ADVERTISEMENT

Karkashin wannan katafaren aiki na ginin layin dogo da kasar Sin ya kammala tun a shekarar 2017, yanzu haka kasar Habasha ta samu babbar damar shigarwa, da fitar da manyan hajoji ta tashoshin jiragen ruwan na Djibouti. Har ma wasu alkaluma sun shaida yadda kaso sama da 95 bisa dari, na hajojin cinikayyar kasar Habasha ke bi ta tashoshin ruwan Djibouti.

Ko shakka babu wannan babban ci gaba ne a tarihin yankin kahon Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Muna iya gani daga sakamakon ci gaban da layin dogon ya haifar, cewa baya ga saukaka safarar hajoji, jiragen kasa dake bin layin dogon, sun kuma saukaka sufurin fasinjoji, ta hanyar rage farashin zirga zirga tsakanin sassan kasashen biyu.

Irin wadannan nasarori da layin dogon ke samu, sun tabbatar da burin da kasar Sin tare da abokan huldar ta na nahiyar Afirka ke fatan cimmawa, ta fuskar gudanar da hadin gwiwa mai dorewa, wanda ke ingiza ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummun kasashe masu tasowa.

Ko shakka ba bu layin dogo na Habasha zuwa Djibouti, na ci gaba da bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, da ma sauran kasashen yankin kahon Afirka, ta fuskar saukaka farashi, da lokacin safarar hajoji, baya ga kara inganta yanayin sufuri, da samar da karin guraben ayyukan yi ga al’ummun kasashen yankin, matakin da masharhanta ke ganin zai ci gaba da fadada cinikayya, da hada hadar shige da fice tsakanin kasashen yankin gabashin Afirka baki daya.

Habasha
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Next Post
Awanni 24 Kafin Rantsarwa, Shugaban Rikon Kwarya A Jihar Yobe Ya Rasu

Awanni 24 Kafin Rantsarwa, Shugaban Rikon Kwarya A Jihar Yobe Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026
Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

July 21, 2026
nema

Guguwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutum Huɗu, Ta Yi Mummunar Ɓarna A Sokoto

July 21, 2026
Hadarin Kwale-Kwale

Mutum Ɗaya Ya Mutu, Sama Da 30 Sun Ɓace A Hatsarin Kwale-kwale A Jigawa

July 21, 2026
ICPC

Badaƙalar Binciken Hukumar Bogi: Gbajabiamila Ya Gurfana Gaban ICPC

July 21, 2026
Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.