• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Waɗanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Waɗanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata, 25 ga Fabrairu, 2025, jaridar LEADERSHIP ta gudanar da bikin karrama waɗanda suka lashe gasar rubuta gajerun labaran soyayya ta Hausa ta hanyar kiran bidiyo na WhatsApp. Wannan gasa an shirya ta ne domin ƙarfafa gwuiwar masu bibiyar LEADERSHIP HAUSA tare da bunƙasa fasahar rubutu a cikin al’ummar masu magana da Hausa.

Taron ya samu halartar jagororin LEADERSHIP, ciki har da Shugaban Sashen Dijital, Mista Samuel Ossai, Editan LEADERSHIP HAUSA, Malam Bello Hamza, Shugaban Sashen LEADERSHIP HAUSA Online, Muhammad Bashir Amin, da kuma Manajan Soshiyal Midiya, Malam Naziru Adam Ibrahim.

  • Wakilin LEADERSHIP Ya Zama Shugaban Wakilan Kafafen Yaɗa Labarai A Kebbi
  • Tinubu Ya Taya Babban Editan LEADERSHIP, Ishiekwene Murnar Cika Shekaru 60

Gasar ta bayar da kyaututtuka na kudi ga waɗanda suka yi nasara: ₦50,000 ga wanda ya zo na farko, ₦25,000 ga wanda ya zo na biyu, da ₦10,000 ga wanda ya zo na uku. Alƙalan gasar, ƙarƙashin jagorancin Muhammad Bashir Amin, sun tantance labarai bisa la’akari da ƙirƙira, asali, da kuma ingancin labari.

A jawabinsa, Editan LEADERSHIP HAUSA, Malam Bello Hamza, ya taya dukkan mahalartan murna tare da karfafa musu gwuiwa kan ci gaba da bibiyar dandalin LEADERSHIP HAUSA. Haka nan, Shugaban Sashen Dijital, Mista Samuel Ossai, ya yaba wa alƙalan gasar da waɗanda suka yi nasara.

Zainab Muhammad, wacce ta zo ta biyu, ta yi jawabi a madadin masu nasarar, inda ta nuna godiyarta ga LEADERSHIP HAUSA bisa wannan dama da suka samu, tare da alƙawarin ci gaba da tallafa wa jaridar a shirye-shiryenta.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

2027: ‘Ku Yi Zaɓe Bisa Ga Ra’ayin Kanku, Ba Lura Da Ƙabila Ko Yanki Ba’, – Atiku Ga ‘Yan Nijeriya

Waɗanda Suka Yi Nasara

1. Aliyu Usman Adam – Matsayi na Ɗaya

Aliyu Usman Adam, ɗan asalin Zariya, Jihar Kaduna, an haife shi a shekarar 1984. Ya kammala karatunsa na firamare da sakandare a Zariya, sannan ya samu digiri a harshen Hausa daga Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, a 2008. Bayan hidimar ƙasa a Jihar Edo, ya yi aiki a kamfanin SAN Yoghurt da kuma Alhuda Center School daga 2011 zuwa 2014.

A 2014, Aliyu ya koma aikin jarida, inda ya yi aiki da jaridar RARIYA a Abuja har zuwa 2017. A halin yanzu, shi ne Manajan shirye-shirye (Content Manager) a Nishadi TV Abuja. Yana da mata da ‘ya’ya biyu.

2. Zainab Muhammad (Indian Girl) – Matsayi Na Biyu

Zainab Muhammad, wacce aka fi sani da “Indian Girl,” ‘yar asalin ƙaramar hukumar Dala ce a Kano. Ta kammala firamare da sakandare a Kano, tare da burin ci gaba da karatun jami’a a nan gaba.

Zainab tana da ƙwazo a ɓangaren ilimin addinin Musulunci, kuma tana amfani da kafafen sada zumunta wajen ilmantarwa da faɗakarwa. A halin yanzu tana da tarin masoya saboda rubuce-rubucenta masu ƙayatarwa da gina al’umma.

3. Mujaheed Nuhu Yusuf (Mujaheed Matashi) – Matsayi Na Uku

Mujaheed Nuhu Yusuf, wanda aka fi sani da Mujaheed Matashin marubuci ne a fagen wasan kwaikwayo kuma mawaki daga Kano. Ya wallafa littattafai biyu na waƙoƙi, ciki har da Philosophy Mysterious Pen, wanda ya wallafa tare da marubuci Haiman Ra’ees.

Mujaheed shi ne shugaban ƙungiyar marubuta Ruhin Adabi, kuma yana wallafa rubuce-rubucensa a shirin Bakandamiya Hikaya da kuma shafinsa na Facebook.

Wannan gasa ta ƙara tabbatar da aniyar LEADERSHIP HAUSA na bunƙasa haɗaka da ƙirƙirar rubutu a cikin al’ummar Hausawa.

Jaridar na shirin ci gaba da shirya irin waɗannan gasar domin ƙarfafa sha’awar adabi da kuma ƙarfafa dangantaka da masu karatu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gajerun LabariLeadership Hausa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Zargin Mourinho Da Furta Kalaman Batanci Akan Galatasaray

Next Post

Sin Ta Jaddada Kudurin Hadin Gwiwa Da Kasa Da Kasa Kan Hakkin Dan Adam

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

52 minutes ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

2027: ‘Ku Yi Zaɓe Bisa Ga Ra’ayin Kanku, Ba Lura Da Ƙabila Ko Yanki Ba’, – Atiku Ga ‘Yan Nijeriya

2 hours ago
Hausa
Labarai

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

2 hours ago
Hausa
Manyan Labarai

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

3 hours ago
Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

4 hours ago
Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?
Labarai

Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

4 hours ago
Next Post
Sin Ta Jaddada Kudurin Hadin Gwiwa Da Kasa Da Kasa Kan Hakkin Dan Adam

Sin Ta Jaddada Kudurin Hadin Gwiwa Da Kasa Da Kasa Kan Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

September 21, 2025
Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

September 21, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

2027: ‘Ku Yi Zaɓe Bisa Ga Ra’ayin Kanku, Ba Lura Da Ƙabila Ko Yanki Ba’, – Atiku Ga ‘Yan Nijeriya

September 21, 2025
Hausa

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

September 21, 2025
Hausa

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 21, 2025
Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

September 21, 2025
Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

September 21, 2025
Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

September 21, 2025
Hausa

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

September 21, 2025
Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

September 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.