• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Mayar Da Kayayyakin Tagulla Na Daular Benin Gida

byCGTN Hausa
2 years ago
Benin

Gidan adana kayayyakin tarihi na Burtaniya, wato the British Museum a Turance, ya kasance daya daga cikin gidajen adana kayayyakin tarihi mafi girma kuma mafi dadadden tarihi a duniya, sai dai da yawa daga cikin kayayyaki sama da miliyan 8 da ke gidan, an kwato ko sato su ne daga kasa da kasa a lokacin da Birtaniya ke mulkin mallaka a sassan duniya. 

Misali a gidan, akwai kayayyakin tagulla kimanin 900 na daular gargajiya ta Benin wadda a zamanin da ta kasance a kudancin kasar Nijeriya, wadanda Burtaniya ta kwaso su gidan bayan da ta wawushe fadar daular a lokacin da ta kaddamar da yaki kan daular a shekarar 1897. Wadannan kayayyakin tagulla dai sun kasance masu matukar muhimmanci a tarihin fasahar Afirka, haka kuma kayayyakin tarihi masu daraja na al’ummar Nijeriya. Ban da su, a gidan, akwai sassakan marmara na Parthenon na kasar Girika, da dutsen Rosetta na kasar Masar da ma wasu kayayyakin tarihi masu daraja dubu 23 da suka fito daga kasar Sin, wadanda suka shaida mummunan tarihin mulkin mallaka na Burtaniya.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kaucewa Aiwatar Da Matakan Da Ka Iya Barazana Ga Tsaronta
  • Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Ga Amurka Game Da Batun Sayarwa Taiwan Makamai

Duk da cewa kasashen Sin da Nijeriya da Girika sun sha bukatar Burtaniya da ta mayar musu da wadannan kayayyakin tarihi, amma kullum Burtaniya ta kan ki bisa dalili na wai “kare lafiyar kayayyakin”. Amma abin kunya shi ne, a cikin kusan shekaru 30 da suka gabata, gidan adana kayayyakin tarihi na Burtaniya wanda ke daukar kanta a matsayin mai kare lafiyar kayayyakin tarihi, ya sha fuskantar sace-sace a kalla sau shida. Wani rahoton bincike na baya-bayan da gidan ya fitar, ya kuma nuna cewa, daga cikin kayayyakin da gidan bai nuna su ba, akwai kimanin 2000 da suka bace ko aka sace su ko kuma suka lalace.

A game da yanayin tsaro na kayayyakin tarihi da ke gidan, Abba Isa Tijani, babban darektan kwamitin kula da gidajen adana kayayyakin tarihi da kayayyakin tarihi na Nijeriya ya ce, “wasu kasashe da gidajen adana kayayyakin tarihi sun sha bayyana mana cewa, kayayyakin tagulla na daular Benin ba su da tsaro a Nijeriya, amma ga yadda aka sace su. Ainihin batun shi ne kayayyakin tarihi ne da aka kwashe, kuma ya kamata a mayar da su gidanjensu ko kasashensu na asali.”

Zamanin mulkin mallaka ya shude, kuma shekaru sama da 120 ke nan da aka kwace kayayyakin tagulla na daular Benin daga Nijeriya, lokaci ya yi da za a mayar da su gida. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu - Minista

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version