ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Mayar Da Kayayyakin Tagulla Na Daular Benin Gida

by CGTN Hausa
2 years ago
Benin

Gidan adana kayayyakin tarihi na Burtaniya, wato the British Museum a Turance, ya kasance daya daga cikin gidajen adana kayayyakin tarihi mafi girma kuma mafi dadadden tarihi a duniya, sai dai da yawa daga cikin kayayyaki sama da miliyan 8 da ke gidan, an kwato ko sato su ne daga kasa da kasa a lokacin da Birtaniya ke mulkin mallaka a sassan duniya. 

Misali a gidan, akwai kayayyakin tagulla kimanin 900 na daular gargajiya ta Benin wadda a zamanin da ta kasance a kudancin kasar Nijeriya, wadanda Burtaniya ta kwaso su gidan bayan da ta wawushe fadar daular a lokacin da ta kaddamar da yaki kan daular a shekarar 1897. Wadannan kayayyakin tagulla dai sun kasance masu matukar muhimmanci a tarihin fasahar Afirka, haka kuma kayayyakin tarihi masu daraja na al’ummar Nijeriya. Ban da su, a gidan, akwai sassakan marmara na Parthenon na kasar Girika, da dutsen Rosetta na kasar Masar da ma wasu kayayyakin tarihi masu daraja dubu 23 da suka fito daga kasar Sin, wadanda suka shaida mummunan tarihin mulkin mallaka na Burtaniya.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kaucewa Aiwatar Da Matakan Da Ka Iya Barazana Ga Tsaronta
  • Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Ga Amurka Game Da Batun Sayarwa Taiwan Makamai

Duk da cewa kasashen Sin da Nijeriya da Girika sun sha bukatar Burtaniya da ta mayar musu da wadannan kayayyakin tarihi, amma kullum Burtaniya ta kan ki bisa dalili na wai “kare lafiyar kayayyakin”. Amma abin kunya shi ne, a cikin kusan shekaru 30 da suka gabata, gidan adana kayayyakin tarihi na Burtaniya wanda ke daukar kanta a matsayin mai kare lafiyar kayayyakin tarihi, ya sha fuskantar sace-sace a kalla sau shida. Wani rahoton bincike na baya-bayan da gidan ya fitar, ya kuma nuna cewa, daga cikin kayayyakin da gidan bai nuna su ba, akwai kimanin 2000 da suka bace ko aka sace su ko kuma suka lalace.

ADVERTISEMENT

A game da yanayin tsaro na kayayyakin tarihi da ke gidan, Abba Isa Tijani, babban darektan kwamitin kula da gidajen adana kayayyakin tarihi da kayayyakin tarihi na Nijeriya ya ce, “wasu kasashe da gidajen adana kayayyakin tarihi sun sha bayyana mana cewa, kayayyakin tagulla na daular Benin ba su da tsaro a Nijeriya, amma ga yadda aka sace su. Ainihin batun shi ne kayayyakin tarihi ne da aka kwashe, kuma ya kamata a mayar da su gidanjensu ko kasashensu na asali.”

Zamanin mulkin mallaka ya shude, kuma shekaru sama da 120 ke nan da aka kwace kayayyakin tagulla na daular Benin daga Nijeriya, lokaci ya yi da za a mayar da su gida. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

 

Benin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Next Post
Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu - Minista

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.