• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Rumbun Bayanai Na Bai-ɗaya A Nijeriya – CGI Isah Jere

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Rumbun Bayanai Na Bai-ɗaya A Nijeriya – CGI Isah Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS) Isah Jere Idris ya yi kiran samar da haɗin kai a tsakanin hukumomin tattara bayanai a ƙasar nan don cimma nasarar samar da rumbun bayanai na bai-ɗaya na Nijeriya domin haɓaka ci gaban ƙasa.

Ya yi wannan kiran ne a hedikwatar hukumar ta shige da fice yayin da yake karɓar baƙoncin tawagar gudanarwa na Shirin Bunƙasa Samar Da Bayanan Shaida Domin Ci Gaba (DID4D) a ziyarar ban girma da suka kai masa.

  • Ba Zan Raga Wa ‘Yan Bindiga Ba Sai Na Ga Bayansu – Buhari 

Sanarwar da ta fito daga Jami’in Sadarwa na NIS, ACI Amos Okpu, ta yi bayanin cewa shugaban hukumar, CGI Isah Jere ya jaddada muhimmiyar rawar da tattara bayanai da sarrafa su za su taka a kan sha’anin tsaro da tsare-tsaren ƙasa.

“Muna rayuwa ne a lokacin da bayanai suka zama wata babbar kadara don ƙarfafa ƙasa kuma haƙiƙa sashen bayanan yana gwagwarmayar ƙwace wa arzikin mai kambunsa na kawo arziki a duniya; don haka akwai bukatar mu haɗa kai don inganta bayanan ƙasa. Ba za mu iya ci gaba da yin watsi da bayananmu suna zaune kara-zube a cikin rumbunan adana su ba a tsakanin hukumomi daban-daban. Lokacin daidaita su su zamo bai-ɗaya ya yi”, in ji shi.

Kwanturola Janar ɗin ya ci gaba da cewa, hukumar a matsayinta na mai taka muhimmiyar rawa a tsarin bayanan ƙasa tun daga shekarar 2019 ta nuna ƙwarin gwiwa wajen cimma daidaiton tsarin bayanan ‘yan ƙasa tare da ɓullo da ingantaccen fasfo na zamani (ePassport) wanda ya wajabta bayar da lambar shaidar ɗan ƙasa (NIN) ga duk mai neman fasfon.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Ya kuma lura cewa hukumar ta NIS tana ci gaba da zuba jari a tsarin tattara bayanai da sarrafa bayanan ta na’urorin da take aiki da su a sassa daban-daban da suka haɗa da Kan Iyakoki don tabbatar da ingantaccen tsarin bayanai. Ya ba da tabbacin cewa NIS za ta ci gaba da kasancewa a shirye a koyaushe don yin haɗin gwiwa tare da hukumomin da abin ya shafa don cimma cikakkiyar daidaituwar bayanan shaida na ƙasa don gudanar da kyawawan tsare-tsare da ci gaban ƙasa.

Bayanai
CGI Isah Idris Jere (a tsakiya) Shugaban Shirin DID4D, Mista Solomon Musa (na biyar daga dama) da sauran mahukuntan shirin da na NIS a yayin ziyarar na haɓaka samar da bayanai

Tun da farko, Babban Jami’in Gudanarwa na DID4D, Mista Solomon Musa Odole ya sanar da cewa tawagarsa ta ziyarci hedkwatar NIS ce don neman haɗin gwiwa kan aikin tantance bayanan shaida a zamanance.

Ya bayyana ƙudirin tawagarsa ta tattaunawa mai ma’ana tare da haɗin gwiwa da NIS don cimma burin Gwamnatin Tarayya na haɓakawa da ƙarfafa tsarin da ake amfani da shi na tattara bayanan shaida da nufin ƙara yawan mutanen da ke da takardar shaidar ƙasa.

A cewarsa, yin hakan zai ƙara sauƙaƙa wa ‘yan ƙasa damar samun muhimman ayyuka, da inganta hanyoyin samar da ayyuka da kuma ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya ta fuskar zamani.

Ya ci gaba da cewa, ana ci gaba da ƙoƙari sosai ciki har da tattaunawa kan manufofin ƙasa da masu ruwa da tsaki wajen samar da dokar kare bayanan sirri ta ƙasa ko sake duba dokokin da ake da su domin tabbatar da cewa an samar da tsare-tsare na hukumomi da suka dace don ciyar da tattalin arzikin ƙasa gaba.

Shirin DID4D dai wani shiri ne na Nijeriya, wanda Bankin Duniya, da Bankin Zuba Jari na Turai da Hukumar Raya Faransa suka ɗauki nauyin gudanar da shi da nufin ƙara yawan mutanen da ke da Lambar Shaida ta ƙasa (NIN) da aka samar ta sahihiyar hanya mai ƙarfi.

  • https://ha.m.wikipedia.org/wiki/Bayanai

Babban jami’in shirin ya samu rakiyar sauran ma’aikatan shirin da suka haɗa da Dakta Walter Duru, Manajan Sadarwa na cikin gida, Bamidele Akinola, Akantan Shirin da Mouktar Adamu, Manajan Sadarwa da dai sauransu.

NIS dai ta duƙufa ka’in da na’in wajen tabbatar da bayanan duk wasu harkoki na shige da fice da suka shafi baƙi da ‘yan ƙasa. Inda ta samar da na’urorin tattara bayanan da tantance su a filayen jiragen sama da iyakokin ruwa da na kan-tudu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Gidaje Da Dama A Kaduna, Suna Sace Jama’a

Next Post

Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

9 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

10 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

12 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

14 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

16 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

17 hours ago
Next Post
Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.