• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Rumbun Bayanai Na Bai-ɗaya A Nijeriya – CGI Isah Jere

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Rumbun Bayanai Na Bai-ɗaya A Nijeriya – CGI Isah Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS) Isah Jere Idris ya yi kiran samar da haɗin kai a tsakanin hukumomin tattara bayanai a ƙasar nan don cimma nasarar samar da rumbun bayanai na bai-ɗaya na Nijeriya domin haɓaka ci gaban ƙasa.

Ya yi wannan kiran ne a hedikwatar hukumar ta shige da fice yayin da yake karɓar baƙoncin tawagar gudanarwa na Shirin Bunƙasa Samar Da Bayanan Shaida Domin Ci Gaba (DID4D) a ziyarar ban girma da suka kai masa.

  • Ba Zan Raga Wa ‘Yan Bindiga Ba Sai Na Ga Bayansu – Buhari 

Sanarwar da ta fito daga Jami’in Sadarwa na NIS, ACI Amos Okpu, ta yi bayanin cewa shugaban hukumar, CGI Isah Jere ya jaddada muhimmiyar rawar da tattara bayanai da sarrafa su za su taka a kan sha’anin tsaro da tsare-tsaren ƙasa.

“Muna rayuwa ne a lokacin da bayanai suka zama wata babbar kadara don ƙarfafa ƙasa kuma haƙiƙa sashen bayanan yana gwagwarmayar ƙwace wa arzikin mai kambunsa na kawo arziki a duniya; don haka akwai bukatar mu haɗa kai don inganta bayanan ƙasa. Ba za mu iya ci gaba da yin watsi da bayananmu suna zaune kara-zube a cikin rumbunan adana su ba a tsakanin hukumomi daban-daban. Lokacin daidaita su su zamo bai-ɗaya ya yi”, in ji shi.

Kwanturola Janar ɗin ya ci gaba da cewa, hukumar a matsayinta na mai taka muhimmiyar rawa a tsarin bayanan ƙasa tun daga shekarar 2019 ta nuna ƙwarin gwiwa wajen cimma daidaiton tsarin bayanan ‘yan ƙasa tare da ɓullo da ingantaccen fasfo na zamani (ePassport) wanda ya wajabta bayar da lambar shaidar ɗan ƙasa (NIN) ga duk mai neman fasfon.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Ya kuma lura cewa hukumar ta NIS tana ci gaba da zuba jari a tsarin tattara bayanai da sarrafa bayanan ta na’urorin da take aiki da su a sassa daban-daban da suka haɗa da Kan Iyakoki don tabbatar da ingantaccen tsarin bayanai. Ya ba da tabbacin cewa NIS za ta ci gaba da kasancewa a shirye a koyaushe don yin haɗin gwiwa tare da hukumomin da abin ya shafa don cimma cikakkiyar daidaituwar bayanan shaida na ƙasa don gudanar da kyawawan tsare-tsare da ci gaban ƙasa.

Bayanai
CGI Isah Idris Jere (a tsakiya) Shugaban Shirin DID4D, Mista Solomon Musa (na biyar daga dama) da sauran mahukuntan shirin da na NIS a yayin ziyarar na haɓaka samar da bayanai

Tun da farko, Babban Jami’in Gudanarwa na DID4D, Mista Solomon Musa Odole ya sanar da cewa tawagarsa ta ziyarci hedkwatar NIS ce don neman haɗin gwiwa kan aikin tantance bayanan shaida a zamanance.

Ya bayyana ƙudirin tawagarsa ta tattaunawa mai ma’ana tare da haɗin gwiwa da NIS don cimma burin Gwamnatin Tarayya na haɓakawa da ƙarfafa tsarin da ake amfani da shi na tattara bayanan shaida da nufin ƙara yawan mutanen da ke da takardar shaidar ƙasa.

A cewarsa, yin hakan zai ƙara sauƙaƙa wa ‘yan ƙasa damar samun muhimman ayyuka, da inganta hanyoyin samar da ayyuka da kuma ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya ta fuskar zamani.

Ya ci gaba da cewa, ana ci gaba da ƙoƙari sosai ciki har da tattaunawa kan manufofin ƙasa da masu ruwa da tsaki wajen samar da dokar kare bayanan sirri ta ƙasa ko sake duba dokokin da ake da su domin tabbatar da cewa an samar da tsare-tsare na hukumomi da suka dace don ciyar da tattalin arzikin ƙasa gaba.

Shirin DID4D dai wani shiri ne na Nijeriya, wanda Bankin Duniya, da Bankin Zuba Jari na Turai da Hukumar Raya Faransa suka ɗauki nauyin gudanar da shi da nufin ƙara yawan mutanen da ke da Lambar Shaida ta ƙasa (NIN) da aka samar ta sahihiyar hanya mai ƙarfi.

  • https://ha.m.wikipedia.org/wiki/Bayanai

Babban jami’in shirin ya samu rakiyar sauran ma’aikatan shirin da suka haɗa da Dakta Walter Duru, Manajan Sadarwa na cikin gida, Bamidele Akinola, Akantan Shirin da Mouktar Adamu, Manajan Sadarwa da dai sauransu.

NIS dai ta duƙufa ka’in da na’in wajen tabbatar da bayanan duk wasu harkoki na shige da fice da suka shafi baƙi da ‘yan ƙasa. Inda ta samar da na’urorin tattara bayanan da tantance su a filayen jiragen sama da iyakokin ruwa da na kan-tudu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Gidaje Da Dama A Kaduna, Suna Sace Jama’a

Next Post

Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

13 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

14 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

18 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.