• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Rumbun Bayanai Na Bai-ɗaya A Nijeriya – CGI Isah Jere

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Lokaci Ya Yi Da Za A Samar Da Rumbun Bayanai Na Bai-ɗaya A Nijeriya – CGI Isah Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS) Isah Jere Idris ya yi kiran samar da haɗin kai a tsakanin hukumomin tattara bayanai a ƙasar nan don cimma nasarar samar da rumbun bayanai na bai-ɗaya na Nijeriya domin haɓaka ci gaban ƙasa.

Ya yi wannan kiran ne a hedikwatar hukumar ta shige da fice yayin da yake karɓar baƙoncin tawagar gudanarwa na Shirin Bunƙasa Samar Da Bayanan Shaida Domin Ci Gaba (DID4D) a ziyarar ban girma da suka kai masa.

  • Ba Zan Raga Wa ‘Yan Bindiga Ba Sai Na Ga Bayansu – Buhari 

Sanarwar da ta fito daga Jami’in Sadarwa na NIS, ACI Amos Okpu, ta yi bayanin cewa shugaban hukumar, CGI Isah Jere ya jaddada muhimmiyar rawar da tattara bayanai da sarrafa su za su taka a kan sha’anin tsaro da tsare-tsaren ƙasa.

“Muna rayuwa ne a lokacin da bayanai suka zama wata babbar kadara don ƙarfafa ƙasa kuma haƙiƙa sashen bayanan yana gwagwarmayar ƙwace wa arzikin mai kambunsa na kawo arziki a duniya; don haka akwai bukatar mu haɗa kai don inganta bayanan ƙasa. Ba za mu iya ci gaba da yin watsi da bayananmu suna zaune kara-zube a cikin rumbunan adana su ba a tsakanin hukumomi daban-daban. Lokacin daidaita su su zamo bai-ɗaya ya yi”, in ji shi.

Kwanturola Janar ɗin ya ci gaba da cewa, hukumar a matsayinta na mai taka muhimmiyar rawa a tsarin bayanan ƙasa tun daga shekarar 2019 ta nuna ƙwarin gwiwa wajen cimma daidaiton tsarin bayanan ‘yan ƙasa tare da ɓullo da ingantaccen fasfo na zamani (ePassport) wanda ya wajabta bayar da lambar shaidar ɗan ƙasa (NIN) ga duk mai neman fasfon.

Labarai Masu Nasaba

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

Ya kuma lura cewa hukumar ta NIS tana ci gaba da zuba jari a tsarin tattara bayanai da sarrafa bayanan ta na’urorin da take aiki da su a sassa daban-daban da suka haɗa da Kan Iyakoki don tabbatar da ingantaccen tsarin bayanai. Ya ba da tabbacin cewa NIS za ta ci gaba da kasancewa a shirye a koyaushe don yin haɗin gwiwa tare da hukumomin da abin ya shafa don cimma cikakkiyar daidaituwar bayanan shaida na ƙasa don gudanar da kyawawan tsare-tsare da ci gaban ƙasa.

Bayanai
CGI Isah Idris Jere (a tsakiya) Shugaban Shirin DID4D, Mista Solomon Musa (na biyar daga dama) da sauran mahukuntan shirin da na NIS a yayin ziyarar na haɓaka samar da bayanai

Tun da farko, Babban Jami’in Gudanarwa na DID4D, Mista Solomon Musa Odole ya sanar da cewa tawagarsa ta ziyarci hedkwatar NIS ce don neman haɗin gwiwa kan aikin tantance bayanan shaida a zamanance.

Ya bayyana ƙudirin tawagarsa ta tattaunawa mai ma’ana tare da haɗin gwiwa da NIS don cimma burin Gwamnatin Tarayya na haɓakawa da ƙarfafa tsarin da ake amfani da shi na tattara bayanan shaida da nufin ƙara yawan mutanen da ke da takardar shaidar ƙasa.

A cewarsa, yin hakan zai ƙara sauƙaƙa wa ‘yan ƙasa damar samun muhimman ayyuka, da inganta hanyoyin samar da ayyuka da kuma ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya ta fuskar zamani.

Ya ci gaba da cewa, ana ci gaba da ƙoƙari sosai ciki har da tattaunawa kan manufofin ƙasa da masu ruwa da tsaki wajen samar da dokar kare bayanan sirri ta ƙasa ko sake duba dokokin da ake da su domin tabbatar da cewa an samar da tsare-tsare na hukumomi da suka dace don ciyar da tattalin arzikin ƙasa gaba.

Shirin DID4D dai wani shiri ne na Nijeriya, wanda Bankin Duniya, da Bankin Zuba Jari na Turai da Hukumar Raya Faransa suka ɗauki nauyin gudanar da shi da nufin ƙara yawan mutanen da ke da Lambar Shaida ta ƙasa (NIN) da aka samar ta sahihiyar hanya mai ƙarfi.

  • https://ha.m.wikipedia.org/wiki/Bayanai

Babban jami’in shirin ya samu rakiyar sauran ma’aikatan shirin da suka haɗa da Dakta Walter Duru, Manajan Sadarwa na cikin gida, Bamidele Akinola, Akantan Shirin da Mouktar Adamu, Manajan Sadarwa da dai sauransu.

NIS dai ta duƙufa ka’in da na’in wajen tabbatar da bayanan duk wasu harkoki na shige da fice da suka shafi baƙi da ‘yan ƙasa. Inda ta samar da na’urorin tattara bayanan da tantance su a filayen jiragen sama da iyakokin ruwa da na kan-tudu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Gidaje Da Dama A Kaduna, Suna Sace Jama’a

Next Post

Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

Related

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF
Labarai

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

10 hours ago
Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 
Labarai

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

16 hours ago
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal
Labarai

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

16 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

17 hours ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

20 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

23 hours ago
Next Post
Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

Kotun Birtaniya Ta Bada Belin Matar Ekeweremadu

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.