• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Da Noman Tumatir

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Lokacin Da Ya Fi Dacewa Da Noman Tumatir
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Da Noman Tumatir
Nijeriya na daya daga cikin kasasen da ke kan gaba wajen noman tumatir, musamman ganin cewa gidaje da dama na amafani da shi.

An fi yin noman tumatir a lokacin kakar rani, inda hakan ya sa ake yawan karancin sa a lokacin kakar damuna, domin kuwa nomansa a lokacin damuna, na da matukar wahala sakamakon yawan lema da ake samu a lokacin.

Ana yin girbin tumatar ne bayan kwana 60 zuwa 90, ya danganta da nau’in wanda aka shuka, ana kuma renon shuka Irinsa daga sati uku zuwa hudu.

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Noman Tumatir:

Takin Gargajiya: Ana so a sanya takin gargajiya a cikin jerin kayan da za a yi amfani da su wajen noman tumatir, haka nan ana so a tabbatar da kasar noman da za a shuka tumatirin na da kyau.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Maganin Feshi: Ya kamata manomi ya tabbatar ya tanadi maganin feshi, don kare tumatirinsa daga harbin kwari ko cututtukan da ke yi masa illa.

Matakan Cin Nasara Wajen Noman Tumatir:
Samar Da Gonar Da Ta Dace:

Samar da gonar da za a noma shi na da matukar kyau, sannan kuma a tabbatar akwai hanya zuwa shiga gonar da fitar da shi a cikin suki zuwa kasuwa.

Daukar Ma’aikata: Ana bukatar a dauki mutane aiki; wadanda za su rika lura da shi, musamman wajen nome shi tare da yi masa feshi.

Ban Ruwa: Yana da kyau a tabbatar da an mallaki kamar rijiyar burtsatsai ko ta bohol a gonar da aka shuka shi, domin yin ban ruwa.
Zabo Ingantaccen Iri: Ana bukatar manomi ya tabbatar ya samo ingantaccen Irin da zai shuka, musamman don samun riba mai yawa.

Ingantaccen Maganin Feshi: Ana so a samu maganin feshin da ya dace da tumatirin da aka shuka, don saurin kashe cutar da ta harbe shi, domin tumatir na fuskantar nau’ikan cututtuka iri daban-daban a lokacin da aka shuka shi.

Sannan kuma, wajibi ne manoninsa ya tabbatar ya kiyaye wajen yin feshin yadda ya dace.

Har ila yau, ana so namomi ya tabbatar da ya kare ganyen tumatar daga taba kasa, don gudun ka da ya lalace.

Lokacin Girbi: Da zarar ya nuna; ana so a gagguata cire shi don gudun ka da ya lalace ko ya rube, sannan bayan girbin an fi so a ajiye yi shi a sarari.

Kasuwancinsa: Kafin shuka tumatir, ana so ka tabbatar ka fara tuntubar masu saye tare da yin bincike kan yadda hada-hadarsa ke tafiya a kasuwanni.

Shin Kana Son Sayar Da Shi A Kasuwa Ko A Manyan Shaguna?

Ya kamata manomi ya yi tunanin a ina ne zai sayar da shi bayan ya girbe shi, domin wasu manoman na kai shi kasuwa ko wasu manyan shaguna; don sayarwa.
Wasu manoman kuma, suna kai shi ne kai tsaye zuwa manyan gidajen sayar da abinci ko otel-otel don sayarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

Next Post

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sassan ‘Yan Kasuwar Sin Da Na Amurka Da Su Bunkasa Amincewa Juna

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

4 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Han

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sassan ‘Yan Kasuwar Sin Da Na Amurka Da Su Bunkasa Amincewa Juna

LABARAI MASU NASABA

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.