ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Da Noman Tumatir

by Abubakar Abba
2 years ago
Tumatir

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Da Noman Tumatir
Nijeriya na daya daga cikin kasasen da ke kan gaba wajen noman tumatir, musamman ganin cewa gidaje da dama na amafani da shi.

An fi yin noman tumatir a lokacin kakar rani, inda hakan ya sa ake yawan karancin sa a lokacin kakar damuna, domin kuwa nomansa a lokacin damuna, na da matukar wahala sakamakon yawan lema da ake samu a lokacin.

Ana yin girbin tumatar ne bayan kwana 60 zuwa 90, ya danganta da nau’in wanda aka shuka, ana kuma renon shuka Irinsa daga sati uku zuwa hudu.

ADVERTISEMENT

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Noman Tumatir:

Takin Gargajiya: Ana so a sanya takin gargajiya a cikin jerin kayan da za a yi amfani da su wajen noman tumatir, haka nan ana so a tabbatar da kasar noman da za a shuka tumatirin na da kyau.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Maganin Feshi: Ya kamata manomi ya tabbatar ya tanadi maganin feshi, don kare tumatirinsa daga harbin kwari ko cututtukan da ke yi masa illa.

Matakan Cin Nasara Wajen Noman Tumatir:
Samar Da Gonar Da Ta Dace:

Samar da gonar da za a noma shi na da matukar kyau, sannan kuma a tabbatar akwai hanya zuwa shiga gonar da fitar da shi a cikin suki zuwa kasuwa.

Daukar Ma’aikata: Ana bukatar a dauki mutane aiki; wadanda za su rika lura da shi, musamman wajen nome shi tare da yi masa feshi.

Ban Ruwa: Yana da kyau a tabbatar da an mallaki kamar rijiyar burtsatsai ko ta bohol a gonar da aka shuka shi, domin yin ban ruwa.
Zabo Ingantaccen Iri: Ana bukatar manomi ya tabbatar ya samo ingantaccen Irin da zai shuka, musamman don samun riba mai yawa.

Ingantaccen Maganin Feshi: Ana so a samu maganin feshin da ya dace da tumatirin da aka shuka, don saurin kashe cutar da ta harbe shi, domin tumatir na fuskantar nau’ikan cututtuka iri daban-daban a lokacin da aka shuka shi.

Sannan kuma, wajibi ne manoninsa ya tabbatar ya kiyaye wajen yin feshin yadda ya dace.

Har ila yau, ana so namomi ya tabbatar da ya kare ganyen tumatar daga taba kasa, don gudun ka da ya lalace.

Lokacin Girbi: Da zarar ya nuna; ana so a gagguata cire shi don gudun ka da ya lalace ko ya rube, sannan bayan girbin an fi so a ajiye yi shi a sarari.

Kasuwancinsa: Kafin shuka tumatir, ana so ka tabbatar ka fara tuntubar masu saye tare da yin bincike kan yadda hada-hadarsa ke tafiya a kasuwanni.

Shin Kana Son Sayar Da Shi A Kasuwa Ko A Manyan Shaguna?

Ya kamata manomi ya yi tunanin a ina ne zai sayar da shi bayan ya girbe shi, domin wasu manoman na kai shi kasuwa ko wasu manyan shaguna; don sayarwa.
Wasu manoman kuma, suna kai shi ne kai tsaye zuwa manyan gidajen sayar da abinci ko otel-otel don sayarwa.

Tumatir
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Han

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sassan ‘Yan Kasuwar Sin Da Na Amurka Da Su Bunkasa Amincewa Juna

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.