• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Filato Sun Fara Yajin Aiki Kan Rashin Biyan Su Albashi

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Ma’aikatan Filato Sun Fara Yajin Aiki Kan Rashin Biyan Su Albashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatan Jihar Filato sun fara yajin aikin sai baba-ta-gani bayan gwamnatin jihar ta kasa biya musu bukatunsu.

An ayyana matakin ne a cikin sanarwar yajin aikin da kungiyar hadin gwiwa ta JNC reshen Filato ta fitar a daren ranar Laraba a Jos.

  • Gwamnati Za Ta Kashe Biliyan 22.44 Kan Ciyar Da Fursunoni A 2023
  • Buhari Ya Nemi Majalisa Ta Sake Amince Masa Ya Ci Bashin Dala Miliyan 800

Sanarwar da Shugaban JNC na Filato, Titus Malau da Sakatare, Timothy Gopep suka sanya wa hannu, ta ce yajin aikin ya biyo bayan karewar wa’adin kwanaki bakwai da gwamnati ta yi wa’adin kwanaki hudu.

Sun ce an sanar da wa’adin da karin wa’adin ne a cikin wasikunsu na ranar 19 ga watan Afrilu, 2023 da 3 ga watan Mayu, 2023.

Jami’an JNC sun bayyana cewa majalisar ta gudanar da taro a ranar 10 ga watan Mayu tare da shugaban ma’aikatan gwamnati da sakataren gwamnatin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

“A bayyane yake cewa gwamnati ba ta nuna isashen kudurin magance matsalolin ba kamar yadda aka gabatar a cikin kundinmu na bukatu kafin wa’adinta ya kare, kamar yadda ta yi alkawari tun farko.

“Duk da haka, bayan ganawar hadin gwiwa tsakanin JNC da shugabannin kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC), an yanke shawarar cewa za a shiga yajin aikin.

“Wannan matakin ya zama wajibi tun da gwamnati ta yi watsi da nata bangaren na yarjejeniyar duk da alkawuran da ta dauka.

“Saboda haka, muna ba da umarnin duk kungiyoyin hadin gwiwarmu da suka fara yajin aikin daga tsakar daren 10 ga Mayu 2023,” in ji su.

A cewarsu, an umurci dukkan kungiyoyin hadin gwiwar da su bi ka’ida tare da tabbatar da cikakken yarda har sai an biya bukatun ma’aikata.

Duo ya yi gargadin cewa duk wani sabawa umarnin zai jawo hukunci mai tsanani.

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya (NAN) ya rawaito cewa ma’aikatan na fafatawa da gwamnatin jihar kan rashin biyan albashi, da dai sauran wasu bukatu da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoJosMa'aikataNUCYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Za Ta Kashe Biliyan 22.44 Kan Ciyar Da Fursunoni A 2023

Next Post

Shugaba Xi Ya Ziyarci Birnin Cangzhou A Lardin Hebei

Related

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

51 minutes ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

3 hours ago
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

4 hours ago
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi
Labarai

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

5 hours ago
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya
Labarai

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

6 hours ago
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

14 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Ziyarci Birnin Cangzhou A Lardin Hebei

Shugaba Xi Ya Ziyarci Birnin Cangzhou A Lardin Hebei

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.