• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Filin Jirgin Saman Legas Sun Shiga Yajin Aiki

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ma’aikatan Filin Jirgin Saman Legas Sun Shiga Yajin Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatan filin jiragen saman Jihar Legas, sun fara yajin aikin gargadi na kwanaki biyu daga ranar Litinin bayan cikar wa’adin sanarwar kwanaki 14 da suka yiwa Ministan Sufuri.

Dalilan da suka haifar da wannan yajin aiki na gargadi da ma’aikatan suke yi sun hada da rashin bayyana sabon tsarin aikinsu wanda aka yi tun shekaru bakwai da suka gabata da kuma batun rushe ofishinsu da ke Legas.

  • Za A Kammala Titin Kaduna Zuwa Kano Kafin Buhari Ya Sauka —Fashola
  • Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 27

Ma’aikatan sun fara yajin aiki a bisa dalilin rashin tabbatar da sabon tsarin aikinsu da kamfanonin jirage hudu suka yi tun shekaru bajwai da suka gabata.

Ma’aikatan sun sanya shinge a kan hanyar shiga cikin filin jirgin ta barin matafiyan cikin gida a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Lagas, matakin da ya dakatar da dukkanin harkoki a filin.

Tun farko dai ma’aikatan sun bada sanarwar shiga yajin aikin kwanaki biyu a ranar Lahadi.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Wannan mataki ya sanya damuwa a zukatan kamfanonin jiragen sama musamman na bangaren yadda zai shafi hada-hadar harkokin fasinjoji lamarin da ya sa wasu cikinsu suka fara tuntunbar shugabannin kungiyoyin ma’aikatan domin kawo karshen sabanin.

Tun a makon da ya gabata, kungiyoyin ma’aikatan suka sanar da mambobinsu a game da shirin da suke yi na shiga yajin aiki na gargadi tsakanin ranar ranar Litinin da kuma ranar Talata, sannan idan har ba a biya musu bukatunsu ba, za su zarce har sai baba ta gani.

Kungiyoyin ma’aikatan jiragen sama biyar ne suka shiga yajin aikin; kuma sun hada da NUATE kungiyar ma’aikatan sifirin jiragen sama ta kasa, sannan akwai kungiyar manyan ma’aikatan harkokin zirga-zirgar jirage ta Nijeriya (ATSSSAN), kungiyar Nijeriya na kwararun ma’aikatan zirga-zirgar jiragen sama (ANAP) da kuma kungiyar matuka jiragen sama da injiniyoyi ta Nijeriya da kuma gamayyar kungiyar ma’aikatan gwamnati da ma’aikatan nishadi ta kasa.

Ma’aikatan sun ce tun farko sun bai wa Ministan sufuri sanarwar kwanaki 14 a ranar 7 ga watan Fabrairu na wannan shekara amma ba a dauki wani mataki ba har sai da wa’adin da suka ba shi ya shude.

Kungiyoyin ma’aikatan suna korafi a game da rashin aiwatar da karin albashin da aka musu da kuma lissafin da ya hau bayan da aka yi wa albashin hukumar NIMET kwaskwarima tun daga 2019 da kuma kin amincewa da fitar da sabon tsarin aikinsu da hukumar albashi na kasa (NSIWC) da kuma ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya (OHCSF) suka ki yi.

Ma’aikatan sufurin jiragen sama sun kaddamar da zanga-zanga a birnin Legas inda rahotanni suke bayyana cewa, hukumomin tsaro sun kama wani dan jarida mai daukar hoto bisa dalilin cewa, ya hallarci zanga-zangar dan gudanar da aikinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Filin Jirgin SamaLegasMa'aikataYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Soki Amurka Bisa Kakabawa Wasu Kamfanoninta Takunkumi Dangane Da Batun Maganin Fentanyl

Next Post

GDPn Sin A Rubu’in Farkon Bana Ya Karu Da Kashi 4.5%

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

7 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
GDPn Sin A Rubu’in Farkon Bana Ya Karu Da Kashi 4.5%

GDPn Sin A Rubu’in Farkon Bana Ya Karu Da Kashi 4.5%

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.