• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Filin Jirgin Saman Legas Sun Shiga Yajin Aiki

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ma’aikatan Filin Jirgin Saman Legas Sun Shiga Yajin Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatan filin jiragen saman Jihar Legas, sun fara yajin aikin gargadi na kwanaki biyu daga ranar Litinin bayan cikar wa’adin sanarwar kwanaki 14 da suka yiwa Ministan Sufuri.

Dalilan da suka haifar da wannan yajin aiki na gargadi da ma’aikatan suke yi sun hada da rashin bayyana sabon tsarin aikinsu wanda aka yi tun shekaru bakwai da suka gabata da kuma batun rushe ofishinsu da ke Legas.

  • Za A Kammala Titin Kaduna Zuwa Kano Kafin Buhari Ya Sauka —Fashola
  • Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 27

Ma’aikatan sun fara yajin aiki a bisa dalilin rashin tabbatar da sabon tsarin aikinsu da kamfanonin jirage hudu suka yi tun shekaru bajwai da suka gabata.

Ma’aikatan sun sanya shinge a kan hanyar shiga cikin filin jirgin ta barin matafiyan cikin gida a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Lagas, matakin da ya dakatar da dukkanin harkoki a filin.

Tun farko dai ma’aikatan sun bada sanarwar shiga yajin aikin kwanaki biyu a ranar Lahadi.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Wannan mataki ya sanya damuwa a zukatan kamfanonin jiragen sama musamman na bangaren yadda zai shafi hada-hadar harkokin fasinjoji lamarin da ya sa wasu cikinsu suka fara tuntunbar shugabannin kungiyoyin ma’aikatan domin kawo karshen sabanin.

Tun a makon da ya gabata, kungiyoyin ma’aikatan suka sanar da mambobinsu a game da shirin da suke yi na shiga yajin aiki na gargadi tsakanin ranar ranar Litinin da kuma ranar Talata, sannan idan har ba a biya musu bukatunsu ba, za su zarce har sai baba ta gani.

Kungiyoyin ma’aikatan jiragen sama biyar ne suka shiga yajin aikin; kuma sun hada da NUATE kungiyar ma’aikatan sifirin jiragen sama ta kasa, sannan akwai kungiyar manyan ma’aikatan harkokin zirga-zirgar jirage ta Nijeriya (ATSSSAN), kungiyar Nijeriya na kwararun ma’aikatan zirga-zirgar jiragen sama (ANAP) da kuma kungiyar matuka jiragen sama da injiniyoyi ta Nijeriya da kuma gamayyar kungiyar ma’aikatan gwamnati da ma’aikatan nishadi ta kasa.

Ma’aikatan sun ce tun farko sun bai wa Ministan sufuri sanarwar kwanaki 14 a ranar 7 ga watan Fabrairu na wannan shekara amma ba a dauki wani mataki ba har sai da wa’adin da suka ba shi ya shude.

Kungiyoyin ma’aikatan suna korafi a game da rashin aiwatar da karin albashin da aka musu da kuma lissafin da ya hau bayan da aka yi wa albashin hukumar NIMET kwaskwarima tun daga 2019 da kuma kin amincewa da fitar da sabon tsarin aikinsu da hukumar albashi na kasa (NSIWC) da kuma ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya (OHCSF) suka ki yi.

Ma’aikatan sufurin jiragen sama sun kaddamar da zanga-zanga a birnin Legas inda rahotanni suke bayyana cewa, hukumomin tsaro sun kama wani dan jarida mai daukar hoto bisa dalilin cewa, ya hallarci zanga-zangar dan gudanar da aikinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Filin Jirgin SamaLegasMa'aikataYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Soki Amurka Bisa Kakabawa Wasu Kamfanoninta Takunkumi Dangane Da Batun Maganin Fentanyl

Next Post

GDPn Sin A Rubu’in Farkon Bana Ya Karu Da Kashi 4.5%

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

19 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

1 day ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

2 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Next Post
GDPn Sin A Rubu’in Farkon Bana Ya Karu Da Kashi 4.5%

GDPn Sin A Rubu’in Farkon Bana Ya Karu Da Kashi 4.5%

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.