• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 15 ga wata, an cika shekaru biyu da tsai da ranar 15 ga watan Maris na kowace shekara a matsayin “ranar duniya ta adawa da kyamar musulunci”. A gun taron MDD na tunawa da ranar da aka gudanar, mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Dai Bing ya gabatar da jawabi, inda ya jaddada cewa, ‘yancin fadin albarkacin baki ba zai iya kare wadanda suka yi kalaman nuna kyama ba, ballantana ma ya zama dalilin gwamnati na rashin daukar matakai. 

A cikin ‘yan shekarun baya, sakamakon tsanancewar rikicin siyasa a tsakanin sassan duniya, wasu ’yan siyasar kasashen yammacin duniya na ta kara tunzura fito na fito tsakanin al’ummu da wayewar kansu. Idan ba a manta ba, sau da dama, wasu tsirarrun ’yan siyasar Turai sun kona Alkur’ani mai tsarki a fili. A bara, yayin da al’ummar musulmi a sassan duniya suka yi shagulgulan babbar sallah, wani abu da ya faru a Turai ya bata yanayin bikin, inda bisa amincewar ’yan sandan wurin, an sake samun wani da ya kona Alkur’ani mai tsarki a wajen wani masallacin da ke birnin Stockholm, babban birnin kasar Sweden. Bayan aukuwar lamarin, kakakin majalisar harkokin wajen Amurka Matthew Miller da ma babban sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg, duk sun bayyana cewa, wannan na daga cikin ’yancin jama’a na fadi albarkacin bakinsu. Sai kuma a watan Janairun shekarar 2017, gwamnatin kasar Amurka ta kaddamar da dokar kayyade shigar da al’ummar kasashen musulmi kasar, matakin da ya sa ta zama kasa daya tilo a duniya da ta sanya haramci kan rukunin al’ummar musulmi. Sai kuma mujallar Charlie Hebdo ta Faransa ta sha wallafa zanen barkwanci da suka tada sabani a tsakanin addinai da kabilu daban daban. Duk wadannan lamura sun tunzura kiyayya a tsakanin mabambantan al’ummu, tare da tsananta rashin fahimtar juna a tsakanin kabilu daban daban, kuma ainihin dalilin da ya sa haka shi ne yadda kasashen yammacin duniya ke nuna bambanci ga irin al’ummun da ba nasu ba, wadanda a ganinsu, wayewar kai na yammacin duniya ya fi na sauran sassan duniya.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Taya Shugaba Putin Na Kasar Rasha Murnar Lashe Zabe
  • Xi Ya Ba Da Umurni Kan Gobarar Da Ta Faru A Birnin Xinyu Na Lardin Jiangxi

Ranar 15 ga wata ta kuma cika shekara daya da kasar Sin ta gabatar da shawarar kiyaye mabambantan wayewar kan duniya, wato Global Civilization Initiative a Turance. Kasancewar kasar Sin kasa ce da ta dade tana samun mabambantan kabilu da addinai da wayewar kai da dama, tana rike da ra’ayi da ya sha bamban sosai da kasashen yamma ta fannin wayewar kan kasashe da kabilu daban daban, wadda a ganinta, duk da bambance bambance da ke tsakanin wayewar kai iri iri, amma babu wani da ya fi wani na daban, don haka ma, kullum take kira da a kiyaye kasancewar mabambantan wayewar kai, tare da sa kaimin yin musaya a tsakaninsu. Sabo da irin wannan akidar martaba mabambantan wayewar kai da kasar Sin ke da shi, a watan Maris na bara, kasar ta gabatar da shawarar kiyaye mabambantan wayewar kai a duniya, inda ta yi kira da a aiwatar da manufofin daidaito, da koyi da juna, da tattaunawa, da tafiya tare tsakanin dukkanin wayewar kan al’ummun duniya, shawarar da ta samu karbuwa daga akasarin kasashen duniya.

A gun wani taron kara wa juna ilmi dangane da shawarar da aka gudanar a farkon bana, mataimakin shugaban jami’ar Abuja Dr. Abdul-Rasheed Na’Allah ya ce, tabbas shawarar za ta samar da kuzari wajen sa kaimin zamanintar da harkokin ‘yan Adam da ma gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya. Kasancewarta kasa mafi yawan al’umma da ma mafi karfin tattalin arziki a nahiyar Afirka, Nijeriya ma na kan hanyar zamanintar da kanta. Dr. Abdul-Rasheed Na’Allah ya ce, “Nijeriya na bukatar yin koyi da mabambantan wayewar kai wajen bunkasa kanta, amma dole ne mu fahimci cewa, ba dole ba ne mu koyi komai daga kasashen yamma domin zamanintar da kanmu.” A ganinsa, ma’anar shawarar nan ita ce ta bayyana wa duniya cewa, kasa da kasa na da ‘yancin zabar tsarin da ya dace da yanayinsu, a yayin da suke da ‘yancin kiyaye al’adun gargajiyarsu.

Akwai kasashe da yankuna sama da 200 a duniyarmu, inda ake samun kabilu sama da 2500, wadanda sabo da bambancin tarihinsu da yanayin kasashensu, suka haifar da mabambantan wayewar kai, kuma hakan ya kara kyautata duniyarmu.(Lubabatu)

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar Sin Na Taimaka Dunkule Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 3

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

13 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

6 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

1 week ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Next Post
BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1

BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 3

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.