• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mafi Karancin Albashi: Gwamnati Ta Buƙaci Ma’aikata Su Karɓi Abin Da Ba Zai Gurgunta Tattalin Arziki Ba

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Mafi Karancin Albashi: Gwamnati Ta Buƙaci Ma’aikata Su Karɓi Abin Da Ba Zai Gurgunta Tattalin Arziki Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) da ta amince da mafi ƙarancin albashi na ƙasa wanda ba zai gurgunta tattalin arzikin ƙasa ba, kuma ya kai ga korar ma’aikata da dama.

Idris ya yi wannan roƙo ne a lokacin da yake buɗe taron ƙungiyar limaman Kirista ta Charismatic Bishops of Nijeriya na 2024 a Abuja ranar Laraba.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 8, Sun Ceto Mutane 87 A Katsina
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Abuja Zuwa Nasarawa

A cikin wata sanarwa da Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabi’u Ibrahim ya fitar, an ruwaito cewa Idris ya jaddada buƙatar samar da ingantaccen tsarin albashi mai ɗorewa wanda zai daidaita buƙatun ma’aikata da yanayin tattalin arzikin ƙasa.

Ya bayyana ƙudirin gwamnati na sake duba mafi ƙanƙantar albashi amma ya yi gargaɗi kan buƙatu da ka iya cutar da tattalin arzikin ƙasar nan.

Ministan ya bayyana ƙoƙarin da gwamnati ke yi na rage tsadar rayuwa da kuma ƙara wa ‘yan Nijeriya ƙarfin yin sayayya ta hanyar shirye-shirye kamar shirin Shugaban Ƙasa na samar da motoci masu aiki da gas (CNG), wanda ke da nufin rage kuɗin sufuri da kashi 50 cikin ɗari.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Ya ce: “Kamar yadda na sha faɗa, Gwamnatin Tarayya ba ta adawa da ƙarin albashi ga ma’aikatan Nijeriya amma muna ci gaba da bayar da shawarwarin samar da ingantaccen tsarin albashi ga ma’aikata – tsarin albashin da ba zai gurgunta tattalin arzikin ƙasa ba har ya kai ga korar ma’aikata da yawa tare da kawo cikas ga jin daɗin ‘yan Nijeriya kusan miliyan 200.

“Muna so ‘yan Ƙungiyar Ƙwadago su fahimci cewa sauƙin da ‘yan Nijeriya ke jira, kuma suka cancanta a ba su, ba zai zo ne kawai ta hanyar ƙarin albashi ba.

“Zai zo ne kuma a ƙoƙarin rage tsadar rayuwa da kuma tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya sun samu ƙarin kuɗaɗe. Kuma a nan ne shirye-shirye kamar shirin CNG na Shugaban Ƙasa ke shigowa.

“Ta hanyar maye gurbin amfani da man fetur da iskar gas, wannan shirin kaɗai zai rage kuɗin sufuri da kashi 50 cikin ɗari.”

Ministan ya yi kira ga malaman addinin Kirista da su goyi bayan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu wajen ganin an farfaɗo da Nijeriya tare da yin addu’ar hikima da jagora a daidai lokacin da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen da ke addabar ta.

“Haƙiƙa, Coci, a tsawon tarihin ƙasar mu, ta kasance abokiyar hulɗa ga gwamnati wajen fafutikar tabbatar da zamantakewa da samar da muhimman ayyukan jin daɗin jama’a kamar asibitoci da makarantu, da kuma cusa ɗabi’u na gari a cikin ‘yan ƙasar mu.

“Ko da muna cikin mawuyacin hali na wucin-gadi amma wanda ya zama dole, ba hutu Shugaban Ƙasa ke yi ba. Ya ƙudiri aniyar tabbatar da cewa an fitar da matakan agaji da dama domin amfanin kowane ɓangare na al’ummar Nijeriya.

“Yanzu, a nan ne ku a matsayin ku na malaman addinin Kirista, a matsayin ku na shugabannin addini da ake mutuntawa da kuma masu faɗa a ji, za ku shigo. A matsayin mu na gwamnati, muna buƙatar goyon bayan ku, shawarwarin ku, da ra’ayoyin ku.

“Abu mafi muhimmanci kuma shi ne muna buƙatar ku san ƙoƙarin da ake yi, da ƙalubalen da ake fuskanta, domin ku taimaka mana mu sanar da waɗannan ikilisiyoyin ku da sauran jama’a.”

Yayin da ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ya hau karagar mulki ne a lokacin da aka fi fuskantar ƙalubale a Nijeriya, Idris ya ce Shugaban Ƙasar na bakin ƙoƙarin sa wajen ganin an samu cigaba mai ɗorewa a faɗin ƙasar nan.

Ya ce: “Babu wanda ke shakkar cewa Shugaban Ƙasa ya tashi tsaye ne tare da jajircewa da aikata abin da ya dace. A cikin shekarar da ta gabata ya aiwatar da muhimman gyare-gyare masu muhimmanci da nufin mayar da ƙasar mu kan turbar haɓaka, wadata, da samun cigaba mai ɗorewa.

“Shugaba Tinubu bai taɓa ƙin amincewa da gaskiyar wannan raɗaɗin da ake ji ba. A cikin jawabin sa na Ranar Dimokiraɗiyya da ya gabatar wa al’ummar ƙasar da safiyar yau, Shugaba Tinubu ya taƙaita shi da kyau da ya ce: ‘Mun ɓullo da gyare-gyare ne domin samar da tushe mai inganci don samun cigaba a nan gaba.

“Babu shakka sauye-sauyen sun haifar da wahalhalu. Amma duk da haka, su ne gyare-gyaren da ake buƙata domin gyara tattalin arziki cikin dogon lokaci ta yadda kowa zai samu damar tattalin arzikin, da samun albashi mai kyau, da kuma ladar ƙoƙarin sa da ayyukan sa.'”

Idris ya ƙara da cewa: “Haƙiƙa, a matsayin mu na al’umma, muna jure wa sadaukarwa na ƙanƙanen lokaci domin samun fa’ida ta dogon lokaci. Mun samu ƙwarin gwiwa da Nijeriyar da ba za a bar kowa a baya ba.”

Ya yi nuni da cewa ma’aikatar sa za ta haɗa kai da malaman Kirista wajen aiwatar da shirin wayar da kan jama’a na ƙasa, wato ‘National Values Charter’.

“Saboda haka, bari in ce Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai za ta yi matuƙar farin ciki da haɗa kai da babban Taron Charismatic Bishops yayin da muke aiwatar da shirin mu na wayar da kan jama’a, wato ‘National Values Charter’, wanda ke neman cusa ɗabi’u masu ɗorewa a cikin zukata da tunanin ‘yan ƙasar mu”, inji shi.

Ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ya aiwatar da manufofin sa na Sabunta Fata yayin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da samun ƙarin nasarori a sassa daban-daban na tattalin arzikin mu.

“Shugaban Ƙasa ya yi aiki tuƙuru don daidaita tattalin arzikin ƙasar ta hanyar janye tallafin man fetur maras ɗorewa da kuma haɗewar kasuwar canjin kuɗaɗe, a matsayin muhimman matakai na karkatar da kuɗaɗe zuwa sassa masu mahimmanci kamar kiwon lafiya, ilimi, da ababen more rayuwa.”

Tun da farko, sai da Shugaban ƙungiyar ‘Charismatic Bishops Conference’ na Ƙasa, Archbishop Leonard Bature Kawas, ya yi alƙawarin biyayya da goyon baya ga gwamnatin Shugaba Tinubu, tare da jaddada cewa za su ci gaba da haɗa kai da gwamnati domin cimma burin ta ga Nijeriya.

Ya ƙara da cewa sun gayyaci ministan wanda Musulmi ne domin ya buɗe taron nasu saboda suna ga cewa ɗan Nijeriya ne mara ƙabilanci wanda ba ya nuna bambancin addini.

Archbishop Kawas ya ce limaman coci daga jihohi 36 na tarayya da ƙasashe 21 ne suka halarci taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kungiyar GwamnoniNlcTUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Bindigar Daji A Dajin Taraba, Sun Ƙwato Makamai Da Kayan Aiki

Next Post

Hukuma A Kano Ta Damƙe Mutane 2 Kan Zargin Zamba

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

2 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

3 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

5 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

7 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

9 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

10 hours ago
Next Post
Hukuma A Kano Ta Damƙe Mutane 2 Kan Zargin Zamba

Hukuma A Kano Ta Damƙe Mutane 2 Kan Zargin Zamba

LABARAI MASU NASABA

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.