• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magana Maras Dacewa Ta Jakada Brigety Na Tare Da Wani Makasudi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Magana Maras Dacewa Ta Jakada Brigety Na Tare Da Wani Makasudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya, Reuben Brigety, jakadan kasar Amurka a kasar Afirka ta Kudu, ya zirgi Afirka ta Kudu da samar da makamai ga kasar Rasha a watan Disamban bara, inda ya ce ya rantse da ransa, abun da ya fada da gaske ne.

Lamarin ya janyo hankalin mutanen duniya, inda shugaban kasar Ukraine da ministar harkokin waje ta kasar Jamus suka fadi ra’ayoyinsu dangane da batun. Sai dai abun da ya abku daga bisani ya nuna cewa, hakika mista Brigety ba shi da wata takamaimiyar shaida.

  • Ministan Wajen Sin Qin Gang Ya Gana Da Takwaransa Na Saliyo David Francis

Bayan da shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya ji zargin da Mista Brigety ya yi wa kasarsa, ya ce bai ji dadin zance maras dacewa da jami’in ya fada ba. Daga baya, ma’aikatar kula da huldar kasa da kasa da hadin gwiwa ta kasar Afirka ta Kudu ta kirawo jakadan na kasar Amurka don yin musayar ra’ayi tare da shi, kana ma’aikatar ta sanar da cewa, Mista Brigety ya yarda da cewa ya yi kuskure, kana ya roki gafara daga gwamnatin kasar Afirka ta Kudu, da jama’ar kasar.

Shi mista Brigety da kansa ma ya sanar a shafin sada zumunta cewa, ya daidaita bahaguwar fahimtar da aka yi kan maganar da ya fada. Sa’an nan, Madam Naledi Pandor, ministar kasar Afirka ta Kudu mai kula da ayyukan huldar kasa da kasa da hadin gwiwa da sauran kasashe, ta tattauna da sakataren harkokin wajen kasar Amurka Tony Blinken ta wayar tarho.

Kana cikin sanarwar da ofishin mista Blinken ya gabatar daga bisani, an jaddada muhimmancin huldar dake tsakanin kasashen nan 2, amma ba tare da yin wani bayani kan zancen mista Brigety ba. Yadda bangaren Amurka ya mayar da martani cikin wani yanayi na kan-kan da kai ya nuna cewa jami’an kasar Amurka sun san kuskurensu. A zahiri ne, yadda jakadan kasar ya yi zargi ba tare da wata shaida ba, har ma ya yi takama cewa zai rantse da rai, bai dace ba ko kadan.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Sai dai an yi zance maras dacewa ne saboda rashin lura? Ko kuma domin wani yunkuri na musamman?
Kamar yadda jaridar Daily Maverick ta kasar Afirka ta Kudu ta bayyana, a watan Faburairun bana, kusan lokacin da sojojin ruwan kasashen Afirka ta Kudu, da Rasha, da Sin suka yi atisaye cikin hadin gwiwa, a yankin teku na kasar Afirka ta Kudu, kasar Amurka ta riga ta gabatar da zargi kan gwamnatin kasar Afirka ta Kudu cewa, ta kwashe wasu makamai cikin wani jirgin ruwan dakon kaya ta kasar Rasha a watan Disamban bara. A sa’i daya, wasu ’yan majalisun kasar Amurka sun bukaci a sake tantance ikon kasar Afirka ta Kudu na halartar shirin dokar tabbatar da karuwar tattalin arziki da damammaki ga kasashen Afirka (AGOA). Wannan shirin doka ya sa kamfanonin kasar Afirka ta Kudu samun gatanci, yayin da suke sayar da kayayyaki zuwa kasar Amurka.

A lokacin, wato watan Faburairu na bana, gwamnatin kasar Afirka ta Kudu ta musunta zirgin da aka yi mata, ta kuma yanke shawarar kaddamar da bincike kan lamarin, gami da tura jami’i mai ba da shawara kan harkar tsaron kasa Sydney Mufamadi zuwa kasar Amurka don tattaunawa da mu’amala da jami’an kasar. Sai dai maganar da jakada Brigety ya fada a wannan karo, ta sa bangaren Afirkta ta Kudu bakin ciki, ganin tamkar kokarin da ta yi na neman daidaita huldar dake tsakaninta da kasar Amurka ya bi ruwa.

A lokacin da mista Mufamadi ke ziyara a kasar Amurka, ya yi kokarin kare ikon kasar Afirka ta Kudu na ci gaba da cin gajiyar shirin dokar AGOA, kana ya tattauna tare da bangaren Amurka dangane da shirin dokar da majalisar wakilan kasar ta zartas a bara, mai taken “Shirin dokar hana kasar Rasha gudanar da munanan ayyuka a nahiyar Afirka”. Makasudin shirin dokar shi ne saka takunkumi kan wasu kamfanoni da kungiyoyi da daidaikun mutane na kasar Rasha, da na wasu kasashen Afirka, don hana kasar Rasha “ zuba jari, da halarta, ko kuma sarrafa harkokin wasu bangarori masu muhimmanci na kasashen Afirka” da “ lahanta moriyar kasar Amurka, da hana ta cimma buri”, wato ana neman hana kasashen Afirka da kasar Rasha yin hadin gwiwa a wasu muhimman harkoki, irinsu hakar ma’adinai, da aikin sadarwa, da aikin soja, da dai sauransu. Har yanzu ba a zartas da shirin dokar a majalisar dattawa ta kasar Amurka ba tukuna. Sai dai idan an zartas da shi, to, zai yi mummunan tasiri kan wasu kasashen Afirka da suke da hulda mai kyau da kasar Rasha, misali kasar Afirka ta Kudu.

Ta hanyar yin tsokaci kan zargin da kasar Amurka ta yi, da wasu shirye-shiryen dokokin da ta gabatar, da lokacin da ta gabatar da su, gami da yadda jakada Brigety ya gabatar da zargi ba tare da wata shaida ba a wannan karo, za a san cewar, dukkan wadannan ayyukan da kasar Amurka ta yi na tare da makasudi guda, wato matsawa kasar Afirka ta Kudu lamba, don hana ta ci gaba da da raya hulda da kasar Rasha. Kana ana neman tsorata sauran kasashe dake nahiyar Afirka, inda tunanin kasar Amurka shi ne, “ Duk wata kasa, ko wata mai karfi kamar Afirka ta Kudu, idan bata bi umarnina ba, to, za a matsa mata lamba, da haifar mata da matsaloli a kai a kai, balle ma sauran kasashe da ba su da karfi.”

Sai dai, manufar kasar Amurka ta babakere, da danniya, da matsawa sauran kasashe lamba, da saka musu takunkumi, ta riga ta zama ruwan dare. Kusan babu wata kasa da ba ta taba shan wahalar manufarta ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisa Ta 10: Tsarin Karba-karba Na Jam’iyyar APC Bai Ma Arewa Adalci Ba

Next Post

An Gurfanar Da Jami’an EFCC 2 Kan Zargin Kisan Abokin Aikinsu 

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

4 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

21 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
An Gurfanar Da Jami’an EFCC 2 Kan Zargin Kisan Abokin Aikinsu 

An Gurfanar Da Jami'an EFCC 2 Kan Zargin Kisan Abokin Aikinsu 

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Brigety

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.